AGC - Hausa

AGC - Hausa AGC HAUSA mallakin Aishub General Concept Ltd ne. Muna ayyuka kamar ɗaukar taruka, labarai, rahoto, jingles, rubuta shirye-shirye, fassara da ayyukan dijital.

A AGC muna maida tunani zuwa kafofin watsa labarai masu ilmantarwa, faɗakarwa da nishaɗantarwa.

🌙 EID MUBARAK 🌙As we celebrate this blessed occasion of Eid, may Allah (SWT) accept our prayers, sacrifices, and acts of...
27/05/2026

🌙 EID MUBARAK 🌙

As we celebrate this blessed occasion of Eid, may Allah (SWT) accept our prayers, sacrifices, and acts of worship. May this season bring peace, happiness, mercy, and countless blessings to every home and family.

A special Eid greeting from Alhaji Sadiq Shuaib Suleiman Dongoro — a symbol of compassion, humanity, and selfless service to society.

May Allah continue to bless our communities with unity, progress, good health, prosperity, and leaders who genuinely care for the people.

Wishing you and your loved ones a joyful and peaceful Eid celebration filled with love, gratitude, and endless blessings.

Eid Mubarak! ✨










’Yan Sintiri a Nasarawa Sun Sha Alwashin Tabbatar da Tsaro a Lokutan Bukukuwan Sallah BabbaDaga Musa Aminu, AbujaBabban ...
26/05/2026

’Yan Sintiri a Nasarawa Sun Sha Alwashin Tabbatar da Tsaro a Lokutan Bukukuwan Sallah Babba

Daga Musa Aminu, Abuja

Babban Kwamandan Ƙungiyar ’Yan Sintiri ta jihar Nasarawa, Godwin Jeyi Ayinda, ya bayyana cewa ƙungiyar za ta ƙara kaimi wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a lokacin gudanar da ibadar Sallar Idi da kuma shagulgulan Babbar Sallah a faɗin jihar.

Kwamanda Ayinda ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai, inda ya ce jami’an ’yan sintiri za su ci gaba da aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da cewa al’umma sun gudanar da bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali da lumana.

Ya yabawa gwamnatin jihar Nasarawa bisa yadda take bai wa ƙungiyar damar isar da koke-kokensu da kuma haɗa kai da su wajen inganta harkokin tsaro a jihar.

A cewarsa, ƙungiyar ba ta nuna bambancin addini, yare ko ƙabila wajen gudanar da ayyukanta, domin babban manufarsu ita ce taimakawa jami’an tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya a dukkan ƙananan hukumomi 13 na jihar Nasarawa.

Haka zalika, Kwamanda Ayinda ya tunasar da Gwamnatin Tarayya kan buƙatar duba kudirin dokar da ke neman tabbatar da ƙungiyar ’yan sintiri a matsayin ɗaya daga cikin hukumomin tsaro na Najeriya.

Ya bayyana cewa amincewa da kudirin zai ƙara ƙarfafa ayyukan ƙungiyar tare da ba ta damar gudanar da aikinta cikin tsari da inganci.

Shugaban ƙungiyar ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro da ’yan sintiri bayanan sirri masu muhimmanci domin taimakawa wajen daƙile ayyukan masu aikata laifi, musamman a tsakanin unguwanni da yankunan karkara na jihar.

Ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin al’umma da jami’an tsaro na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar Nasarawa da Najeriya baki ɗaya.









Ƙungiyar Kwararrun Matasan Kirista Na Arewacin Najeriya Ta Gargadi Kan Ƙaruwar Ƙungiyoyin Kare Kai, Ta Nemi Faɗaɗa Shiri...
26/05/2026

Ƙungiyar Kwararrun Matasan Kirista Na Arewacin Najeriya Ta Gargadi Kan Ƙaruwar Ƙungiyoyin Kare Kai, Ta Nemi Faɗaɗa Shirin Dakarun Tsaron Gandun Daji

Ƙungiyar Kwararrun Matasan Kirista Na Arewacin Najeriya (NCYP) ta bayyana damuwa kan yadda matsalar tsaro ke ci gaba da yaɗuwa a Najeriya, musamman yadda ’yan ta’adda ke amfani da dazuka da yankunan da ba su da cikakken tsaro wajen kai hare-hare da sake dawowa bayan jami’an tsaro sun kore su.

A cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Isaac Abrak, ya sanya wa hannu, kungiyar ta yabawa rundunar sojin Najeriya bisa ƙoƙarin da take yi wajen yaƙar ’yan ta’adda, amma ta gargadi gwamnati cewa korar miyagu daga dazuka ba tare da samar da tsarin tsaro na dindindin ba na sa su sake dawowa su kai sababbin hare-hare.

Kungiyar ta ce saboda gibin tsaro da jinkirin amsa matsalolin tsaro a wasu yankuna, al’ummomi da dama sun fara kafa ƙungiyoyin kare kai, masu gadi da kungiyoyin mafarauta domin kare rayukansu da dukiyoyinsu.

NCYP ta bayyana cewa irin wannan lamari ya taba faruwa a wasu ƙasashe irin su Iraq, Mali da Burkina Faso, inda al’umma s**a kafa ƙungiyoyin tsaro na kansu saboda matsin lambar hare-haren ’yan ta’adda.

Sai dai kungiyar ta yi gargadin cewa idan ba a tsara irin wadannan ƙungiyoyi cikin tsarin tsaro na ƙasa ba, hakan na iya haifar da rikice-rikice da matsalolin shugabanci a nan gaba.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa akwai wasu manyan dazuka da miyagu ke amfani da su wajen motsi tsakanin jihohi, ciki har da dazukan Rugu, Birnin Gwari, Kamuku da Kuyambana, wanda hakan ke bai wa masu aikata laifi damar tsallake iyakokin jihohi domin kauce wa jami’an tsaro.

A saboda haka, kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya, Hedikwatar Tsaro, Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta faɗaɗa shirin Dakarun Tsaron Gandun Daji da ake gwadawa a wasu jihohi zuwa faɗin Najeriya baki ɗaya.

A cewar kungiyar, tsarin Dakarun Tsaron Gandun Daji zai taimaka wajen kare yankunan da aka kwato daga hannun ’yan ta’adda, inganta tattara bayanan sirri, ƙarfafa sa ido a dazuka, da kuma rage nauyin da ke kan rundunar sojin Najeriya da ke fama da matsalolin tsaro a sassa daban-daban na ƙasar.

Kungiyar ta jaddada cewa jinkirta ɗaukar matakin faɗaɗa tsarin Dakarun Tsaron Gandun Daji na iya ƙara jefa ƙasar cikin matsalolin tsaro masu wahalar magancewa a nan gaba.










26/05/2026

GMBNI Ta Kai Ziyara Tsangayar Malam Umar Bagobiri a Nasarawa, Ta Yi Addu’ar Zaman Lafiya Ga Najeriya

Daga Musa Aminu, Abuja

Gidauniyar Inganta Rayuwar ’Yan Najeriya Tun Daga Tushe (GMBNI) ta kai ziyara ta musamman zuwa Tsangayar Malam Umar Bagobiri da ke Anguwar Nasiru Soja a Maraba, ƙaramar hukumar Karu ta jihar Nasarawa, domin ci gaba da ayyukan wayar da kai da gina al’umma.

Shugabar gidauniyar, Dr. Fatima Mohammed Goni, ta bayyana cewa ziyarar na daga cikin shirye-shiryen haɗin gwiwa da gidauniyar ta ƙulla da Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Najeriya (NDLEA), musamman wajen yaƙi da matsalolin da s**a shafi miyagun ƙwayoyi da lalacewar tarbiyya a tsakanin matasa.

Ta ce gidauniyar na mai da hankali wajen wayar da kai, ƙarfafa tarbiyya da kuma haɗa kan al’umma domin samar da zaman lafiya da cigaba mai ɗorewa a ƙasa.

A yayin ziyarar, an gudanar da addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban Najeriya, tare da roƙon Allah Ya kare ƙasar daga matsalolin rashin tsaro da sauran ƙalubalen da ke addabar al’umma.

A nashi jawabin, Malam Umar Bagobiri yabawa ya yi da ƙoƙarin gidauniyar GMBNI da kuma haɗin gwiwar da take yi da NDLEA wajen ƙarfafa kyawawan ɗabi’u da yaƙi da miyagun ƙwayoyi a tsakanin al’umma.









RANAR ARFA: RANAR RAHAMA, GAFARA DA ‘YANTUWA DAGA WUTARanar Arfa na daga cikin mafi falala a cikin kwanakin shekara a Mu...
25/05/2026

RANAR ARFA: RANAR RAHAMA, GAFARA DA ‘YANTUWA DAGA WUTA

Ranar Arfa na daga cikin mafi falala a cikin kwanakin shekara a Musulunci. Rana ce ta rahama, amsa addu’a, gafarar zunubai da kusanci zuwa ga Allah Maɗaukakin Sarki.

A wannan rana mai albarka, miliyoyin alhazai kan tsaya a filin Arfa suna roƙon Ubangiji cikin tawali’u da hawaye, yayin da sauran Musulmai a faɗin duniya ke azumi, zikiri, addu’a da neman gafara.

Manzon Allah (SAW) ya bayyana cewa babu ranar da Allah ke ‘yanta bayinsa daga wuta kamar ranar Arfa. Haka kuma azumin ranar Arfa yana kankare zunuban shekara guda da ta gabata da kuma shekara mai zuwa.

Mu yi amfani da wannan rana wajen: • Tuba ta gaskiya
• Yawaita istigfari
• Yin addu’a ga kanmu da iyalanmu
• Neman zaman lafiya da albarka ga ƙasa
• Taimakon mabukata da kyautatawa mutane

Allah Ya sa mu dace da falalar ranar Arfa, Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya kuma sa mu cikin bayinsa na gari. Amin.










25/05/2026

Alhamdulillah

“Shekaru 13 Al’ummar Zaria Na Cikin Jarrabawar Wakilcin ’Yan Amshin Shata” — Hon. Jume Danmori DamboDaga Musa Aminu, Abu...
22/05/2026

“Shekaru 13 Al’ummar Zaria Na Cikin Jarrabawar Wakilcin ’Yan Amshin Shata” — Hon. Jume Danmori Dambo

Daga Musa Aminu, Abuja

Ɗan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna mai wakiltar mazabar Zaria Kewaye ƙarƙashin jam’iyyar ADC, Honarabul Jume Danmori Dambo, ya bayyana cewa al’ummar mazabar sun shafe shekaru sama da 13 suna fama da matsalar rashin ingantaccen wakilci a majalisa.

Dan takarar ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da GTR Hausa a Kaduna, inda ya ce abin da ya fi damunsa shi ne yadda wasu wakilai ke zama tamkar “’yan amshin shata” maimakon wakilan jama’a masu kare muradun al’umma.

A cewarsa, wannan hali ne ya sa ya yanke shawarar komawa fagen siyasa domin kawo sauyi da kuma ceto al’ummar mazabar daga matsin rashin wakilci nagari.

Hon. Danmori Dambo ya ce a baya ya taɓa janyewa daga fafutukar siyasa na wani lokaci, amma yadda yake ganin matsalolin da al’umma ke ci gaba da fuskanta ba tare da samun murya mai ƙarfi a majalisa ba, ya sa ya ga babu makawa sai ya dawo domin bayar da tasa gudummawar.

Ya bayyana cewa majalisa ya kamata ta kasance wurin kare haƙƙin jama’a da gabatar da muradunsu, ba wajen bin son rai ko amfanin wasu tsiraru ba.

A cewarsa:

“Na ga cewa idan na ci gaba da zura ido ba tare da na ɗauki mataki ba, to Allah zai tambaye ni a kan abin da zan iya yi domin taimakon al’umma amma na ƙi.”

Danmori ya kuma yi kira ga al’ummar Zaria Kewaye da su tsaya tsayin daka wajen zaɓar shugabanni masu gaskiya, kishin jama’a da hangen nesa, domin samun ci gaba mai ɗorewa a mazabar da jihar baki ɗaya.

Ya jaddada cewa burinsa shi ne samar da wakilci na gari da zai mayar da hankali kan matsalolin matasa, ilimi, ayyukan yi, ci gaban al’umma da kuma kare muradun talakawa a Majalisar Dokokin Jihar Kaduna.

Wane fata kuke yi masa?











Babbar Kotun Tarayya Ta Tsawaita Wa’adin Gabatar da Kundin Rajistar Mambobin Jam’iyyun Siyasa Zuwa Satumban 2026Babbar K...
22/05/2026

Babbar Kotun Tarayya Ta Tsawaita Wa’adin Gabatar da Kundin Rajistar Mambobin Jam’iyyun Siyasa Zuwa Satumban 2026

Babbar Kotun Tarayya ta soke wa’adin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanya wa jam’iyyun siyasa domin gabatar da kundin rajistar mambobinsu, tare da tsawaita wa’adin zuwa watan Satumban shekarar 2026.

Tun da farko, INEC ta umarci jam’iyyun siyasa da su gabatar da cikakken kundin sunayen mambobinsu da bayanansu kafin ranar 10 ga watan Mayu domin samun damar shiga babban zaɓen shekarar 2027.

Sai dai hukuncin da Babbar Kotun Tarayyar ta yanke yanzu ya bai wa jam’iyyun siyasa damar ci gaba da tattara bayanan mambobi da gudanar da rajista har zuwa watan Satumban 2026.

Masu sharhi kan harkokin siyasa sun bayyana cewa wannan mataki zai bai wa jam’iyyun ƙarin lokaci domin inganta tsarin rajista, ƙara yawan mambobi, da kuma tabbatar da cika ka’idojin da ake buƙata kafin zaɓen 2027.











Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Goyon Bayanta Ga Ci gaban Kafofin Yaɗa Labarai da Raya Al’adu a Taron RATTAWUMinistan Yaɗa...
22/05/2026

Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Goyon Bayanta Ga Ci gaban Kafofin Yaɗa Labarai da Raya Al’adu a Taron RATTAWU

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na ci gaba da tallafa wa cibiyoyi da ƙungiyoyin ƙwararru da ke taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa harkokin yaɗa labarai, raya al’adu da masana’antar fasaha a Najeriya.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin taron ƙaddamar da taswirar shirye-shiryen bikin cika shekaru 50 da kafuwar Ƙungiyar Ma’aikatan Rediyo, Talabijin, Wasan Kwaikwayo da Fasaha ta Najeriya (RATTAWU), wanda aka gudanar a Abuja.

Mohammed Idris ya bayyana RATTAWU a matsayin muhimmiyar ƙungiya da ta ba da gagarumar gudunmawa wajen cigaban sadarwa, wayar da kai, da raya al’adun Najeriya tsawon shekaru da dama.

Ya jaddada muhimmancin sadarwa mai inganci, aikin jarida na gaskiya da ɗa’a, da kuma wayar da kan jama’a kan yadda ake tantance sahihan bayanai, domin ƙarfafa dimokuraɗiyya, haɗin kan ƙasa, da yaƙi da yaɗuwar labaran ƙarya a wannan zamani na kafafen sadarwa na zamani.

Ministan ya ƙara da cewa kafafen yaɗa labarai na da muhimmiyar rawa wajen gina ƙasa da ilmantar da al’umma, yana mai kira ga ‘yan jarida da masu aikin watsa shirye-shirye da su ci gaba da mutunta gaskiya, adalci, kishin ƙasa da ƙa’idojin sana’a a dukkan ayyukansu.

Haka kuma ya yaba wa RATTAWU bisa yadda ta tsaya tsayin daka wajen kare muradun ma’aikatan kafafen yaɗa labarai da masu fasaha, tare da inganta ƙwarewa da bunƙasa harkokin al’adu a Najeriya cikin shekaru 50 da s**a gabata.

Taron ya samu halartar shugabannin ƙungiyoyi, jami’an gwamnati, ƙwararrun ‘yan jarida, da masu ruwa da tsaki daga masana’antar fasaha da sadarwa, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen bikin cika shekaru 50 na ƙungiyar.











AL'ADA, ADDINI DA GASKIYAR ZUCIYA: ABIN DA YA KAMATA MU DUBAA wani shiri da aka gabatar a gidan rediyo, wani mutum ya ta...
21/05/2026

AL'ADA, ADDINI DA GASKIYAR ZUCIYA: ABIN DA YA KAMATA MU DUBA

A wani shiri da aka gabatar a gidan rediyo, wani mutum ya tambayi Malam Ibrahim Khalil game da wata matsala da yake fuskanta a wurin aikinsa. Ya bayyana cewa yana aiki ne a wata ƙungiya tare da mutane daga sassa daban-daban na ƙasar nan, ciki har da mata daga kudancin Najeriya, waɗanda idan s**a haɗu da shi suke miƙa hannu domin gaisuwa.

Ya ce yana amsa gaisuwar ne cikin ladabi da mutuntawa, amma daga baya sai ya rika jin nadama da damuwa a zuciyarsa.

Da yake ba da amsa, Malam Ibrahim Khalil ya bayyana cewa idan gaisuwar ba ta sha’awa ba ce, kuma al’ada ce ta mu’amala da mutuntawa a wurin aiki, to bai kamata mutum ya shiga damuwa ko tsananta wa kansa ba. Ya ƙara da cewa kin amsa irin wannan gaisuwa a wasu lokuta na iya sa a ɗauki mutum a matsayin mai raini ko rashin mutunta wasu.

Malam ɗin ya kawo misali da yadda shugabannin ƙasashe kan yi mu’amala da juna a tarukan ƙasa da ƙasa, inda wani lokaci mace za ta miƙa hannu domin gaisuwa, kuma rashin amsawa zai iya haifar da matsala ta fuskar diflomasiyya ko mutunci.

Sai dai wannan batu ya sake tayar da tunani mai zurfi kan yadda al’umma ke yawan mayar da hankali ga abin da ake gani a zahiri, tare da yin watsi da abin da yake ɓoye a zukata da ayyukan sirri.

A wasu lokuta, idan wani shugaba ko fitaccen mutum ya gaisa da mace cikin mutunci da ladabi, sai a ga ana masa s**a da zargi kamar ya aikata babban laifi. Amma a lokaci guda, ana samun munanan laifuffuka irin na cin zarafin yara da fyade daga wasu mutanen da a zahiri ake kallonsu a matsayin masu tsananin addini ko kamun kai.

Abin takaici ne yadda kotuna da hukumomin tsaro ke ci gaba da fuskantar yawaitar shari’o’in fyade da cin zarafin ƙananan yara mata da maza. Wannan na nuna cewa gyaran al’umma ba ya tsaya ga abin da ake nunawa a fili kawai, illa yana buƙatar tsoron Allah na gaskiya, tarbiyya, tsaftar zuciya, da kyawawan ɗabi’u.

Addini ya koyar da kamun kai, mutunci da kiyaye iyakoki, amma bai koyar da riya ko fakewa da addini domin ɓoye munanan ɗabi’u ba. Haka kuma, akwai buƙatar al’umma su daina gaggawar hukunta mutane bisa abin da s**a gani a zahiri kawai, tare da manta cewa mafi muhimmanci shi ne gaskiyar zuciya da kyawawan ayyuka.

Dole ne mu fahimci cewa mutunci, ladabi da kyakkyawar mu’amala ba laifi ba ne idan ana yin su cikin tsari da tsafta. Haka kuma, wajibi ne mu fi mayar da hankali wajen yaƙi da ainihin munanan ɗabi’u da laifuffukan da ke lalata rayuwar yara da tarbiyyar al’umma, maimakon yawan ce-ce-ku-ce kan abubuwan da ake yi cikin mutunci da ladabi.

Al’umma mai lafiya ita ce wadda ke haɗa tarbiyya, ilimi, tsoron Allah da kuma gaskiyar zuciya. Domin ba duk wanda ya nuna tsauri a zahiri ba ne yake da tsarkin zuciya, haka kuma ba duk wanda ya yi mu’amala cikin ladabi da mutane ba ne yake da muguwar niyya.

Allah Ya tsare zukatanmu, Ya ba mu fahimtar addini ta gaskiya, Ya kuma kare al’umma daga dukkan nau’ikan cin zarafi da munanan ɗabi’u. Ameen.












𝗔𝗦𝗨𝗨 𝗥𝗲𝘀𝗵𝗲𝗻 𝗞𝗮𝗻𝗼 𝗧𝗮 𝗬𝗶 𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵-𝗪𝗮𝗱𝗮𝗿𝗮𝗶 𝗗𝗮 𝗥𝗮𝘀𝗵𝗶𝗻 𝗖𝗶𝗸𝗮𝗸𝗸𝗶𝘆𝗮𝗿 𝗔𝗶𝘄𝗮𝘁𝗮𝗿 𝗗𝗮 𝗬𝗮𝗿𝗷𝗲𝗷𝗲𝗻𝗶𝘆𝗮𝗿 𝟮𝟬𝟮𝟱Daga Yusuf Bala, KanoƘungiyar Mala...
21/05/2026

𝗔𝗦𝗨𝗨 𝗥𝗲𝘀𝗵𝗲𝗻 𝗞𝗮𝗻𝗼 𝗧𝗮 𝗬𝗶 𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵-𝗪𝗮𝗱𝗮𝗿𝗮𝗶 𝗗𝗮 𝗥𝗮𝘀𝗵𝗶𝗻 𝗖𝗶𝗸𝗮𝗸𝗸𝗶𝘆𝗮𝗿 𝗔𝗶𝘄𝗮𝘁𝗮𝗿 𝗗𝗮 𝗬𝗮𝗿𝗷𝗲𝗷𝗲𝗻𝗶𝘆𝗮𝗿 𝟮𝟬𝟮𝟱

Daga Yusuf Bala, Kano

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), reshen Kano, ta nuna matuƙar damuwa tare da yin Allah-wadai da abin da ta bayyana a matsayin rashin cikakkiyar aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Gwamnatin Tarayya da ƙungiyar a shekarar 2025, musamman dangane da biyan albashi da alawus-alawus ga malaman jami’o’i.

Shugaban ASUU na yankin Kano, Dakta Abdullahi Muhammad, ne ya bayyana hakan yayin ganawarsa da manema labarai a sakatariyar ƙungiyar da ke tsohuwar jami’ar Bayero Kano ranar Laraba.

Ya ce ƙungiyar na Allah-wadai da yadda wasu shugabannin jami’o’i ke aiwatar da yarjejeniyar ta hanyar biyan wani ɓangare na haƙƙoƙin malaman, ko kuma kin biya gaba ɗaya, duk da tanade-tanaden da aka amince da su a yarjejeniyar.

A cewarsa, tun bayan fara aiwatar da yarjejeniyar a ranar 14 ga Janairu, 2026, malaman jami’o’i sun nuna haƙuri da fahimta, amma yanzu akwai alamun cewa gwamnatin na nuna halin ko-in-kula wajen tabbatar da cikakken aiwatar da abin da aka cimma.

Dakta Abdullahi Muhammad ya bayyana damuwa kan rashin kafa kwamitin sa ido da zai tabbatar da bin diddigin yadda ake aiwatar da yarjejeniyar domin kauce wa tsaiko da sabani.

Ya kuma soki yadda ake aiwatar da yarjejeniyar ba tare da tsari iri ɗaya ba a jami’o’in ƙasar, yana mai cewa wasu shugabannin jami’o’i suna zaɓar ɓangarorin da za su aiwatar, musamman kan batun alawus-alawus na koyarwa, karin aiki da kuma na farfesoshi.

Shugaban ASUU na Kano ya jaddada cewa waɗannan alawus ya kamata su kasance cikin tsarin albashin malamai ana biyansu a kai a kai kamar yadda yarjejeniyar ta tanada.

Ƙungiyar ta kuma yi kira ga gwamnatocin tarayya da jihohi da su mutunta yarjejeniyar domin tabbatar da zaman lafiya da daidaito a jami’o’in Najeriya, tare da kauce wa duk wani tsaiko da ka iya janyo tangarda ga harkokin karatu.

Ya tunatar da cewa tattaunawar da ta kai ga cimma yarjejeniyar ta ɗauki kusan shekaru takwas, daga 2017 zuwa 2025, saboda haka bai dace a yi wasa da abin da aka amince da shi ba.

Dakta Abdullahi Muhammad ya yi gargadin cewa haƙurin da malaman jami’o’i suke nunawa ya fara kai wa matakin ƙarshe, yana mai cewa mambobin ƙungiyar za su iya ɗaukar matakin da s**a dace idan gwamnati ta ci gaba da nuna halin ko-in-kula wajen aiwatar da yarjejeniyar.

Me zaku ce?











Address

Abuja

Telephone

+2348099441477

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AGC - Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AGC - Hausa:

Share