21/05/2026
AL'ADA, ADDINI DA GASKIYAR ZUCIYA: ABIN DA YA KAMATA MU DUBA
A wani shiri da aka gabatar a gidan rediyo, wani mutum ya tambayi Malam Ibrahim Khalil game da wata matsala da yake fuskanta a wurin aikinsa. Ya bayyana cewa yana aiki ne a wata ƙungiya tare da mutane daga sassa daban-daban na ƙasar nan, ciki har da mata daga kudancin Najeriya, waɗanda idan s**a haɗu da shi suke miƙa hannu domin gaisuwa.
Ya ce yana amsa gaisuwar ne cikin ladabi da mutuntawa, amma daga baya sai ya rika jin nadama da damuwa a zuciyarsa.
Da yake ba da amsa, Malam Ibrahim Khalil ya bayyana cewa idan gaisuwar ba ta sha’awa ba ce, kuma al’ada ce ta mu’amala da mutuntawa a wurin aiki, to bai kamata mutum ya shiga damuwa ko tsananta wa kansa ba. Ya ƙara da cewa kin amsa irin wannan gaisuwa a wasu lokuta na iya sa a ɗauki mutum a matsayin mai raini ko rashin mutunta wasu.
Malam ɗin ya kawo misali da yadda shugabannin ƙasashe kan yi mu’amala da juna a tarukan ƙasa da ƙasa, inda wani lokaci mace za ta miƙa hannu domin gaisuwa, kuma rashin amsawa zai iya haifar da matsala ta fuskar diflomasiyya ko mutunci.
Sai dai wannan batu ya sake tayar da tunani mai zurfi kan yadda al’umma ke yawan mayar da hankali ga abin da ake gani a zahiri, tare da yin watsi da abin da yake ɓoye a zukata da ayyukan sirri.
A wasu lokuta, idan wani shugaba ko fitaccen mutum ya gaisa da mace cikin mutunci da ladabi, sai a ga ana masa s**a da zargi kamar ya aikata babban laifi. Amma a lokaci guda, ana samun munanan laifuffuka irin na cin zarafin yara da fyade daga wasu mutanen da a zahiri ake kallonsu a matsayin masu tsananin addini ko kamun kai.
Abin takaici ne yadda kotuna da hukumomin tsaro ke ci gaba da fuskantar yawaitar shari’o’in fyade da cin zarafin ƙananan yara mata da maza. Wannan na nuna cewa gyaran al’umma ba ya tsaya ga abin da ake nunawa a fili kawai, illa yana buƙatar tsoron Allah na gaskiya, tarbiyya, tsaftar zuciya, da kyawawan ɗabi’u.
Addini ya koyar da kamun kai, mutunci da kiyaye iyakoki, amma bai koyar da riya ko fakewa da addini domin ɓoye munanan ɗabi’u ba. Haka kuma, akwai buƙatar al’umma su daina gaggawar hukunta mutane bisa abin da s**a gani a zahiri kawai, tare da manta cewa mafi muhimmanci shi ne gaskiyar zuciya da kyawawan ayyuka.
Dole ne mu fahimci cewa mutunci, ladabi da kyakkyawar mu’amala ba laifi ba ne idan ana yin su cikin tsari da tsafta. Haka kuma, wajibi ne mu fi mayar da hankali wajen yaƙi da ainihin munanan ɗabi’u da laifuffukan da ke lalata rayuwar yara da tarbiyyar al’umma, maimakon yawan ce-ce-ku-ce kan abubuwan da ake yi cikin mutunci da ladabi.
Al’umma mai lafiya ita ce wadda ke haɗa tarbiyya, ilimi, tsoron Allah da kuma gaskiyar zuciya. Domin ba duk wanda ya nuna tsauri a zahiri ba ne yake da tsarkin zuciya, haka kuma ba duk wanda ya yi mu’amala cikin ladabi da mutane ba ne yake da muguwar niyya.
Allah Ya tsare zukatanmu, Ya ba mu fahimtar addini ta gaskiya, Ya kuma kare al’umma daga dukkan nau’ikan cin zarafi da munanan ɗabi’u. Ameen.