Arewa Traders Associations

Arewa Traders Associations Arewa Traders Associations is an umbrella of all legitimate traders in the 19 State Northern Nigeria.

02/05/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN!

Cikin alhini da jimami Ƙungiyar Arewa Traders Associations ke miƙa saƙon ta’aziyya ga Alhaji Musbahu Umar Maizare, ɗaya daga cikin mambobin Board of Trustees na ƙungiyar, bisa rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Yahanasu Umar Maizare.

Allah Ya yi mata rasuwa, muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta mata, Ya jiƙanta da rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarta. Allah Ya haskaka ƙabarinta, Ya yalwata mata rahama da gafara, Ya kuma ba iyalai da dukan waɗanda ta bari haƙurin jure wannan babban rashi.

In Sha Allah, za a gudanar da sallar jana’izarta da safiyar yau Asabar da ƙarfe 11:00 na safe a gidanta da ke Yanshuni, titin Unguwar Alkali dake Jihar Katsina.

Muna roƙon ‘yan uwa da abokan arziki da su taimaka da addu’o’i domin neman rahama da gafarar Allah a gareta.

Allah Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura kuranta, Ya sa Aljanna ce makomarta. Amin Ya Allah.

ZIYARAR SHUGABANNIN ƘUNGIYAR ƳAN KASUWAR AREWA ZUWA OFISHIN MD NA JAIZ TAKAFULA jiya ne shugabannin Ƙungiyar Ƴan Kasuwar...
30/04/2026

ZIYARAR SHUGABANNIN ƘUNGIYAR ƳAN KASUWAR AREWA ZUWA OFISHIN MD NA JAIZ TAKAFUL

A jiya ne shugabannin Ƙungiyar Ƴan Kasuwar Arewa s**a kai wata muhimmiyar ziyara ta musamman zuwa ofishin Manajan Darakta (MD) na Jaiz Takaful, Alhaji Ibrahim Shehu.

An gudanar da wannan ziyara ne domin tattauna hanyoyin da tsarin inshorar Musulunci (Takaful) zai amfani ƴan kasuwar Arewa da sauran al’umma baki ɗaya. Haka kuma, an tattauna muhimman batutuwa da s**a haɗa da tsarin gidauniyar Jaiz Takaful da kuma manufar Ta’awun (Ta’aweed) a tsarin Musulunci, wadda ke ƙarfafa taimakekeniya da tallafawa juna.

Wadanda s**a halarci ziyarar sun haɗa da:

Alhaji Adamu Hassan Ibrahim National President, Arewa Traders Association
Alhaji Tukur Abubakar Deputy National President
Alhaji Abdulazeez Vice Secretary
Alhaji Dahiru Manigi Organising Secretary
Hajiya Hadiza Women Leader
Alhaji Bawa Head of Security

Shugabannin sun bayyana cewa wannan ziyara wani mataki ne na samar wa ƴan kasuwar Arewa ci gaba da amfanoni masu ɗorewa ta hanyar tsarin Jaiz Takaful wanda ya dace da koyarwar addinin Musulunci.

ZIYARA TA MUSAMMAN ZUWA JAMI'AR MALIK KHALID! Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu.Bayan kammala ibadarsa a ƙa...
06/04/2026

ZIYARA TA MUSAMMAN ZUWA JAMI'AR MALIK KHALID!

Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Bayan kammala ibadarsa a ƙasar Saudiyya, Shugaban Ƙungiyar Arewa Traders Association na ƙasa, Alhaji Adamu Hassan Ibrahim, ya samu damar kai ziyara ta musamman zuwa Jami’ar Malik Khalid da ke birnin Abha, wani gari da ke da tazarar kusan kilomita 800 daga Birnin Makka.

Jami’ar Malik Khalid na daga cikin manyan jami’o’in ƙasar Saudiyya, kuma tana da ɗalibai sama da dubu sittin. Daga cikin waɗannan ɗalibai, akwai sama da dubu huɗu daga ƙasashen waje, yayin da ɗaliban da s**a fito daga nahiyar Afirka s**a haura dubu biyu da ɗari shida.

A yayin ziyarar, ya samu damar ganawa da ƙungiyar ɗaliban Najeriya da ke karatu a wannan jami’a, waɗanda yawansu ya haura mutum ɗari biyu da hamsin. A cikinsu akwai ɗaliban digirin digirgir (PhD), na digirin biyu (Master’s), da kuma na digirin farko (Degree).

Ya tattauna da ɗaliban kan makomarsu bayan sun kammala karatu idan s**a dawo gida Najeriya, tare da jaddada muhimmancin su kasancewa masu kawo ci gaba, sauyi na ilimi, da bunƙasa rayuwar al’umma. Hakika, amfanin ilimi shi ne idan ya amfani mai shi, sannan ya amfani al’ummarsa.

Alhamdulillah, ɗaliban Najeriya masu karatun digirin digirgir (PhD) a jami’ar sun haura mutum talatin, yayin da masu karatun Master’s s**a zarce mutum hamsin.

Haka kuma, shugabannin jami’ar sun tarbe mu cikin matuƙar girmamawa da karamci. Sun shirya mana kyakkyawar liyafa, tare da bayyana aniyarsu ta ci gaba da ba da cikakken goyon baya ga ɗaliban Najeriya da ke karatu a jami’ar.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara ɗaukaka wannan jami’a, Ya albarkaci ɗalibanmu, Ya ba su nasara a karatunsu da rayuwarsu baki ɗaya, Ya kuma sa su zama sanadin ci gaban ƙasarmu da al’ummarmu.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'AUN!A madadin shugabannin wannan ƙungiya da daukacin mabiyanta, muna miƙa saƙon ta'aziy...
04/04/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'AUN!

A madadin shugabannin wannan ƙungiya da daukacin mabiyanta, muna miƙa saƙon ta'aziyyarmu ga iyalan marigayi Dr. Tahir Muhammad, National President na Amalgamated Union of Foodstuff and Cattle Dealers of Nigeria (AUFCDN), bisa rasuwarsa.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya jikansa da rahama, Ya sanya Aljannar Firdausi ta zama makomarsa. Haka kuma muna roƙon Allah Ya bai wa iyalansa, abokansa, da al'ummar Jihar Kano haƙurin jure wannan babban rashi.

Marigayi Dr. Tahir Muhammad ya rasu ne jiya sakamakon hatsarin mota a hanyarsa ta dawowa daga Kano zuwa Abuja. An gudanar da jana'izarsa yau da misalin ƙarfe 11:00 na safe a gidansa da ke Kano.

Allah Ya gafarta masa, Ya kuma gafarta wa sauran 'yan'uwa Musulmai da s**a riga mu gidan gaskiya. Amin.

A madadin kungiyar ’yan kasuwan Arewa, muna mika sakon ta’aziyya mai cike da jimami da alhini ga Malam Nasir El-Rufai da...
30/03/2026

A madadin kungiyar ’yan kasuwan Arewa, muna mika sakon ta’aziyya mai cike da jimami da alhini ga Malam Nasir El-Rufai da daukacin iyalansa bisa rasuwar mahaifiyarsa.

Hakika wannan babban rashi ne wanda ya tabo zukatanmu. Muna rokon Allah Madaukakin Sarki Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarta.
Mu na rokon Allah ya bawa iyalai da sauran ƴan uwa hakurin jure wannan babban rashi.

18/03/2026

Gaisuwar Ta'aziyya da jajantawa ga al'ummar jihar Borno.

Alh Adamu Hassan Ibrahim
National President Arewa Traders Association

06/03/2026

Gudumawar da Ƙungiyar Ƴan Kasuwar Arewa ta bayar wajen zaɓen Gwamnatin nan, har yanzu kwalya bata biya kuɗin sabulu ba.


Alhaji Adamu Hassan Ibrahim
National President Arewa Traders Association

KISAN GILLA: Ƙungiyar ƴan kasuwa ta jihar Filato ta buƙaci mambobin ta su zauna a gida ranar Alhamis Daga: Unity Radio F...
25/02/2026

KISAN GILLA: Ƙungiyar ƴan kasuwa ta jihar Filato ta buƙaci mambobin ta su zauna a gida ranar Alhamis

Daga: Unity Radio FM/TV Jos

Ƙungiyar ƴan kasuwa ta jihar Filato, wato Plateau State Traders and Marketers Association, ta aiyana ranar Alhamis, 26 ga watan Fabrairun 2026 a matsayin ranar zaman makokin ƴan kasuwar su da maharan Birom s**a kashe a kan hanyar neman abin dogaro da kai.

Ƙungiyar, reshen Jos Ta Arewa, ta buƙaci duk wani ɗan kasuwa dake Jos ta Arewa ya zauna a gida a ranar Alhamis ɗin daga ƙarfe 6 na safe zuwa 4 na yamma.

Sakataren ƙungiyar na jiha, Alhaji Sabo Adamu ne ya bayyana hakan, yayin zantawa da tashar Unity FM yau Laraba a cikin shirin “Jirgin Unity”.

Ƙungiyar, ta bakin shugaban ta na Jos ta Arewa, Sama'ila Garba da sakataren ƴan kasuwar Terminus, Sulaiman Yusuf, ta kuma buƙaci al'umma su kwantar da hankalin su, inda tace matakin nata ba ya na nufin tashin hankali bane, illa takaicin “rashin kirkin” da ɓata gari s**a yiwa mambobin su.

📸: TRUST

24/02/2026

In a shocking escalation of Plateau State's cycle of violence, Berom Christian youths have been accused of targeting and killing innocent Muslim travellers on the Jos–Shendam highway during a February 23, 2026, protest blockade over recent killings in Barkin Ladi and Dorowa Babuje. What began as a demonstration against the deaths of 10 community members reportedly turned deadly, with Muslim travellers singled out. According to social media accounts, some travellers were killed, and the head of one victim was chopped off by rampaging Berom Christians killers.

Fatima Abdullahi, Jakadiyan Matan Dorawa Bubuje from the Muslim Community, poured out her anguish on Facebook: “Raise up an Talk About what's happening in Barkin ladi an Dorowa babuje The killing is too much our love ones are been taking away from us ,our husbands, Children's, Friends and Relatives are being murdered without any reason what's our crime is it because we are villagers , wallahi even if this will be my last chance living on earth I must speak out Enough is Enough to the killing, we the women are always left with orphans no help no nothing,our children are always raised by a single mother's no school,no food,no Shelter,Their life's always end up being so miserable , our children end up their lives on the street, Haba Have a pity on us always taken the life of our husbands living us an our children in boundage , Allah ya Isa mana wallah...”

Adding fuel to the outrage, another Facebook user, Auwalu Moosa Auwalu Bros, demanded immediate federal intervention: “justice must be served, these innocent travellers they face this inhumane act because they were muslim, grumesoly murdered by berom killers we call federal government to take decisively action.”

A disturbing lifeless body of one of the innocent Muslim travellers killed is attached in the comment section: viewers discretion is advised.

16/02/2026

ZANGA-ZANGAR ADAWA DA ‘YAN AREWA A GARIN PORT HARCOURT!

Jiya, ‘yan kasuwar Arewa da ke zaune a Igwuruta, cikin garin Port Harcourt, Jihar Rivers, sun fuskanci hare-hare ba tare da wata hujja ba daga wasu bata-gari a cikin birnin. Bayan lalata shagunan su, wasu matasa sun shirya wata zanga-zanga da s**a kira da “Aboki Must Go”, suna kira ga ‘yan Arewa da su bar jihar.

An ce matasan masu zanga-zangar sun yi zargin cewa kashe-kashen da sace-sacen mutane da ke faruwa a Port Harcourt ‘yan Arewa ne ke haddasawa, duk da cewa da yawa daga cikinsu suna gudanar da halalcin kasuwancinsu cikin lumana.

Hare-haren da aka kai ba tare da hujja ba da kuma lalata dukiyoyin ‘yan Arewa wadanda suke kira da “Aboki” ko “Malam” na iya kasancewa sakamakon yadda kafafen yada labarai ke yi musu mummunan fassara da kuma yadda ake kallon Musulmi da wani salo na tsangwama da ƙyara a ƙasa baki ɗaya. Masu zanga-zangar sun yi watsi da kasancewar ‘yan dabar su, masu bautar gumaka, masu garkuwa da mutane, da sauran masu aikata laifukan fasadi a cikin al’ummominsu, sai s**a ɗora laifin gaba ɗaya kan Hausawa ‘yan Arewa.

Bayan hare-haren da aka kai kan ‘yan kasuwar Arewa a Port Harcourt, muna kira ga Gwamnati da ta ɗau Mataimakin da ya dace a kudancin ƙasar nan, Idan ba haka ba Arewa ba zata ci gaba da zira ido ana cin mutuncin ƴan Arewa a kudancin ƙasar nan ba, wannan ne magana ta gaskiya a yi nazari sosai a kai.

Najeriya ta kowa ce. A jihohin Arewa kamar Kano, Kaduna, Abuja da Sokoto, Bauchi, Katsina, Borno da sauran jihohin Arewa miliyoyin ‘yan Kudu na rayuwa, suna aiki, kuma suna gudanar da Kasuwancin su da Addini su cikin nasara ba tare da an kai musu hari ko tsangwama ba saboda asalinsu, kabilarsu ko addininsu. Ana daukar su a matsayin ‘yan Najeriya kamar kowa, ba baki ba.

Abubuwa da dama sun faru a Arewa shekaru da dama ƴan kudu mazauna Arewa suna satan yaran mu yan Arewa su kai su kudu tare da sauya masu Addini, amma hakan bata sa mun dauki mataki akan su a jihohin da abin ya faru ba, sai muka bar ma hukuma aikin ta.

Dora laifi a kan jama’a gaba ɗaya abu ne mai hadari kuma rashin adalci ne. Laifi ba shi da kabila, addini ko yanki. Idan aka rika kai hari kan ‘yan kasuwa marasa laifi saboda asalinsu ko abin da s**a yi imani da shi, hakan yana raunana hadin kan kasa kuma yana haifar da ƙiyayya wadda ba ta amfani ga kowa.

Idan akwai damuwar tsaro ta gaskiya, hanyar da ta dace ita ce a yi aiki tare da jami’an tsaro da shugabannin al’umma ba kai hari ga ‘yan kasa masu zaman lafiya da ke neman rufin asiri ba.

Tattaunawa, hadin kai da bin doka su ne kaɗai hanyoyin da za su tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.

Mu zabi haɗin kai maimakon rarrabuwa, adalci maimakon son zuciya, da zaman tare cikin lumana maimakon gaba. Karfin Najeriya yana cikin bambance-bambancen ta, kuma kare juna ko da wane ne mutum nauyi ne da ya rataya a wuyan mu baki ɗaya.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI’UN! 😥A mamadin shugabanin wannan kungiya da mabiyanta na mika sakon ta’aziyya da alhini...
15/02/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI’UN! 😥

A mamadin shugabanin wannan kungiya da mabiyanta na mika sakon ta’aziyya da alhini bisa mummunar gobarar da ta tashi a Kasuwar Singa dake Kano, wacce ta haddasa asarar dukiyoyi masu yawa ga ‘yan kasuwa da al’ummar yankin baki daya.

Wannan lamari abin takaici ne matuka, domin ya shafi rayuwar dubban ‘yan kasuwa da iyalansu. Muna jajantawa ga duk wanda wannan ibtila’i ya rutsa da shi, muna rokon Allah (SWT) Ya maye musu da alkhairi fiye da abin da s**a rasa, Ya kuma kiyaye afkuwar irin haka nan gaba.

A matsayinta na kungiya mai kishin ci gaban ‘yan kasuwa, Arewa Traders Association na kira ga hukumomi da masu ruwa da tsaki da su gaggauta daukar matakan bincike tare da samar da hanyoyin kariya domin hana sake faruwar irin wannan gobara a kasuwanninmu.

Haka kuma muna kira ga Gwamnatin jihar Kano da ta tarayya da kuma daukacin al’umma da ‘yan uwa ‘yan kasuwa da su hada kai wajen tallafawa wadanda abin ya shafa, domin rage musu radadin wannan asara a dai dai lokacin da a ke daf da shiga watan Ramadan.

Allah ya maida masu da mafi alkhairi ya kuma kiyaye faruwar hakan nan gaba. Ameen.

Sanarwa daga:
Arewa Traders Association

Address

Utako By Abraham Plaza Beside ABC Park
Abuja
900108

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Traders Associations posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Traders Associations:

Share