16/02/2026
ZANGA-ZANGAR ADAWA DA ‘YAN AREWA A GARIN PORT HARCOURT!
Jiya, ‘yan kasuwar Arewa da ke zaune a Igwuruta, cikin garin Port Harcourt, Jihar Rivers, sun fuskanci hare-hare ba tare da wata hujja ba daga wasu bata-gari a cikin birnin. Bayan lalata shagunan su, wasu matasa sun shirya wata zanga-zanga da s**a kira da “Aboki Must Go”, suna kira ga ‘yan Arewa da su bar jihar.
An ce matasan masu zanga-zangar sun yi zargin cewa kashe-kashen da sace-sacen mutane da ke faruwa a Port Harcourt ‘yan Arewa ne ke haddasawa, duk da cewa da yawa daga cikinsu suna gudanar da halalcin kasuwancinsu cikin lumana.
Hare-haren da aka kai ba tare da hujja ba da kuma lalata dukiyoyin ‘yan Arewa wadanda suke kira da “Aboki” ko “Malam” na iya kasancewa sakamakon yadda kafafen yada labarai ke yi musu mummunan fassara da kuma yadda ake kallon Musulmi da wani salo na tsangwama da ƙyara a ƙasa baki ɗaya. Masu zanga-zangar sun yi watsi da kasancewar ‘yan dabar su, masu bautar gumaka, masu garkuwa da mutane, da sauran masu aikata laifukan fasadi a cikin al’ummominsu, sai s**a ɗora laifin gaba ɗaya kan Hausawa ‘yan Arewa.
Bayan hare-haren da aka kai kan ‘yan kasuwar Arewa a Port Harcourt, muna kira ga Gwamnati da ta ɗau Mataimakin da ya dace a kudancin ƙasar nan, Idan ba haka ba Arewa ba zata ci gaba da zira ido ana cin mutuncin ƴan Arewa a kudancin ƙasar nan ba, wannan ne magana ta gaskiya a yi nazari sosai a kai.
Najeriya ta kowa ce. A jihohin Arewa kamar Kano, Kaduna, Abuja da Sokoto, Bauchi, Katsina, Borno da sauran jihohin Arewa miliyoyin ‘yan Kudu na rayuwa, suna aiki, kuma suna gudanar da Kasuwancin su da Addini su cikin nasara ba tare da an kai musu hari ko tsangwama ba saboda asalinsu, kabilarsu ko addininsu. Ana daukar su a matsayin ‘yan Najeriya kamar kowa, ba baki ba.
Abubuwa da dama sun faru a Arewa shekaru da dama ƴan kudu mazauna Arewa suna satan yaran mu yan Arewa su kai su kudu tare da sauya masu Addini, amma hakan bata sa mun dauki mataki akan su a jihohin da abin ya faru ba, sai muka bar ma hukuma aikin ta.
Dora laifi a kan jama’a gaba ɗaya abu ne mai hadari kuma rashin adalci ne. Laifi ba shi da kabila, addini ko yanki. Idan aka rika kai hari kan ‘yan kasuwa marasa laifi saboda asalinsu ko abin da s**a yi imani da shi, hakan yana raunana hadin kan kasa kuma yana haifar da ƙiyayya wadda ba ta amfani ga kowa.
Idan akwai damuwar tsaro ta gaskiya, hanyar da ta dace ita ce a yi aiki tare da jami’an tsaro da shugabannin al’umma ba kai hari ga ‘yan kasa masu zaman lafiya da ke neman rufin asiri ba.
Tattaunawa, hadin kai da bin doka su ne kaɗai hanyoyin da za su tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.
Mu zabi haɗin kai maimakon rarrabuwa, adalci maimakon son zuciya, da zaman tare cikin lumana maimakon gaba. Karfin Najeriya yana cikin bambance-bambancen ta, kuma kare juna ko da wane ne mutum nauyi ne da ya rataya a wuyan mu baki ɗaya.