03/05/2026
A Ranar Mauludin Imam Ridha (AS):
Sashen Harisawa masu kula da bangaren kiwon lafiya (Hurras Medical Team) sun bayar da agaji a ciki da wajen Nijeriya don tunawa da ranar haihuwar Imam Ridha (AS), limami na takwas a cikin limaman shiriya (AS).
Bangaren, sun ayyana ranar ta haihuwar Imam Ridha (AS), wanda ya kasance likitan likitoci, wato ranar 11 ga watan Zulƙa'ada, a matsayin “Ranar Ƙungiyar Ma’aikatan Lafiya ta Ƙasa” (National Medical Team Day) a bangaren na Harisawa, inda suke burin a duk shekara za su rika bayar da agaji na musamman ga mabukata a cikinta.
A yayin gudanar da ayyukan ranar, HMT sun gudanar da ayyukan tsaftace muhallai, ziyarar asibitoci, duben marasa lafiya, yankan farce da aski (kyauta) da kuma raba kyaututtuka ga duk waɗanda s**a ziyarta a ranar. An gudanar da ayyukan ne a Zones 10 daga cikin 14 da ake da su a faɗin aikin na Harisanci.
1. A Rasulul Akram Zone, Harisawan sun gudanar da yankan farce da aski kyauta tare da raba kyaututtuka ga al'umma a matsayin ayyukan wannan ranar.
2. Haka a Amirulmumin (AS) Zone, Harisawan sun ziyarci Primary Health Care Centre da ke Yalwan Kagadama, inda s**a tsaftace muhallin tare da duba marasa lafiyar da ke kwance a wurin.
3. Zone din Azzahra (AS) ma ba a bar su a baya ba, sun buɗe ajin karatu ne don karantarwa kan sha'anin kiwon lafiya.
4. Imam Husaini (AS) Zone sun gudanar da ayyukan tsaftace muhallai tare da yi wa al'umma aski kyauta.
5. Zone ɗin Imam Baqir (AS) sun gudanar da wankin ciwo ga waɗanda suke da rauni, da kuma gwajin BP (Blood Pressure) ga al'umma kyauta.
6. A Zone ɗin Imam Musa Al-Kazeem (AS) kuma, Harisawan sun ziyarci makarantar allo a Jalingo Unit, da kuma ziyarar asibiti a Gombe Unit.
7. Haka Zone ɗin Imam Aliyu Ridha (AS) sun ziyarci tsangayar almajirai inda s**a wayar musu kai akan muhimmancin kula da tsafta.
8. A Zone ɗin Imam Jawad (AS) kuwa, Harisawan sun gudanar da aikin tsaftace muhallai da share wuraren da suke tara datti da ƙazanta.
9. Zone ɗin Imam Aliyu Al-Hadi (AS) ma ba a bar su a baya ba, sun ziyarci makarantar allo, inda s**a wayar musu kai kan muhimmancin kula da lafiya, tare da raba musu kyautar Omo don su tsaftace tafafinsu.
10. A Zone ɗin Imam Mahadi (AF) kuwa, Harisawan sun ziyarci asibiti don duba marasa lafiyar da ke kwance a wajen, tare da raba musu kyaututtuka.
Wannan rana ba kawai rana ce ta masu kula da kiwon lafiya ba, sai dai rana ce ta nuna ƙauna da sada zumunci tsakanin al'ummar da ke rayuwa a muhalli guda. Cikin taimakon Allah, duk wurin da aka ziyarta ko aka gudanar musu da wani aiki, sun mayar da martani ne da addu'o'i na neman kariya da lafiya ga Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), wanda shi ne ya nusar da Harisawan irin wannan aiki.
Hurras Medical Team na ƙara kira ga al'umma da su riƙa lura da abincin da suke ci, ruwan da suke sha, muhallin da suke zama, da kuma tsaftar kayan da suke sakawa don kula da lafiyarsu. Yin hakan zai taimaka sosai wajen rage kamuwa da cututtuka a cikin al'umma.
Saƙo daga Hurras Medical Team,
— Hurrasul Harakatil Islamiyya
15 Zulƙa'ada, 1447
03/05/2026