29/08/2025
In dai kana bukatar haske a dunia da lahira, Matsayi da alkairi, nutsuwar zuciya, Dan’uwa ka guji shirka, ka mika wuya ga Allah.
Game da shirka Ubangiji Ya mana kashedi
Yana gayawa Ma’aiki ﷺ Ya sanar da mu.
“Hakika kuma an yi maka wahayi Kai da wadanda s**a gabace ka cewa: “Tabbas idan ka yi shirka lallai aikinka zai baci, kuma tabbas za ka kasance daga cikin asararru.
“A’a’ Allah kadai zaka bauta wa, ka kuma kasance daga masu godiya.”
Qur’an (Az-zumar 65/66)
Babu abin da babu a taskar Allah, Kar ka biyewa tarkon bokaye da matsafa, da wasun mu suke bi. babu abin da za su iya yima face su kaika su baro. Allah yafi kusa damu.
Ubangiji (SWT) Ya fada a Qur’ani
“Kuma idan bayiNa sun tambaye ka game da Ni, to Ni kusa Nake (da su) ina amsa kiran mai kira Idan ya kiraye Ni. to su amsa Mini nawa kiran, kuma su yi imani da Ni. don su Shiryu.” Qur’an (Al-Bakara 186)
Ubangiji Ka shiryar da mu da zuri’armu. Amin.
Barkanmu da Jumu’ah. &