ANNUR-Hausa

ANNUR-Hausa Wannan Sahihiyar kafar watsa ingantattun labarai ce daga da sasssan duniya....

BABBAR MAGANA : Wata budurwa ta rasa aikin da ake biyanta sama da naira dubu 200 a wata bayan ta ki amincewa da cire hij...
18/05/2026

BABBAR MAGANA : Wata budurwa ta rasa aikin da ake biyanta sama da naira dubu 200 a wata bayan ta ki amincewa da cire hijabinta kamar yadda kamfanin da take aiki ya bukata.

Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama ke yabawa matashiyar bisa tsayawa kan addininta da mutuncinta duk da rasa damar aikin.

Yayin da wasu ke ganin ya kamata a mutunta ‘yancin addini a wuraren aiki, wasu kuma sun bayyana cewa kamfanoni na da dokoki da ma’aikata ke bi.

Mutane da dama sun yi mata addu’ar Allah Ya maye mata da aikin da ya fi wannan alheri da albarka. 🤲

Wanne fata za ku yi mata?

Ku shiga shafin jaridar ANNUR-Hausa domin samun Sahihan Labarai.

Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano ta dakatar da wasu fitattun jaruman Kannywood guda biyu, Amina Uba Hassan...
17/05/2026

Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano ta dakatar da wasu fitattun jaruman Kannywood guda biyu, Amina Uba Hassan da Adam Garba da aka fi sani da Raba Gardama, daga gudanar da harkokin fim a jihar har na tsawon shekara ɗaya.

Hukumar ta bayyana cewa ta ɗauki matakin ne bayan bayyanar jaruman a wani bidiyo da ta ce ya saɓa da tarbiyya kuma ya haddasa ce-ce-ku-ce a tsakanin al’ummar jihar Kano.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya fitar a safiyar Lahadi, ya ce dakatarwar na cikin ƙoƙarin tsaftace tarbiyya da tabbatar da bin dokokin hukumar a masana’antar Kannywood.

Sanarwar ta ƙara da cewa dokar hukumar ta bai wa hukumar ikon dakatar da duk wani ɗan masana’antar fim da ya karya ƙa’idojinta, tare da gargadin cewa karya umarnin dakatarwar na iya jawo hukunci mai tsauri a ƙarƙashin doka.

Da yake jawabi kan lamarin, shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, ya yi kira ga jarumai da sauran masu ruwa da tsaki a Kannywood da su guji duk wani abu da ka iya zubar da mutuncin masana’antar ko kawo mata rashin kima a idon al’umma.

Hukumar ta kuma buƙaci producers da directors na masana’antar Kannywood da su mutunta umarnin dakatarwar, tana mai cewa yin watsi da shi tamkar ƙalubalantar dokar hukumar ne kai tsaye.

Da ɗumi-ɗumi: Ɗan Marigayi Buhari, Yusuf Buhari, Ya Lallasa Abokin Takara Da Kuri’u 5,849 A Zaɓen Fidda Gwani Na jam’iyy...
16/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: Ɗan Marigayi Buhari, Yusuf Buhari, Ya Lallasa Abokin Takara Da Kuri’u 5,849 A Zaɓen Fidda Gwani Na jam’iyyar APC

Yusuf Muhammadu Buhari, ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya samu gagarumar nasara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress domin neman kujerar majalisar wakilai ta mazaɓar Sandamu/Daura/Mai’adua.

Yusuf Buhari ya samu kuri’u 5,849 inda ya lallasa Hon. Auwal Lawal Daura wanda ya samu kuri’u 21 kacal.

Sakamakon zaɓen ya tayar da kura a siyasar jihar Katsina, yayin da magoya bayan APC da matasa ke bayyana wannan nasara a matsayin babban karɓuwa da Yusuf Buhari ya samu daga al’ummar yankin.

Masu sharhi na ganin nasarar na iya ƙara ƙarfin tasirin gidan Buhari a siyasar Najeriya musamman a jihar Katsina.
👀 Shin wannan nasara alama ce cewa Yusuf Buhari zai gaji tasirin siyasar mahaifinsa a Arewa?

Tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa diyarsa ta taba roƙonsa da ya hada kai da tsohon ɗan takarar ...
12/05/2026

Tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa diyarsa ta taba roƙonsa da ya hada kai da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, a lokacin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da ARISE News a ranar Litinin, inda yake magana kan yadda matasa ke sauya tunaninsu a harkokin siyasa.

Karin bayani 👉🏽 https://premierradio.ng/e9fm

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa, tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Ali Pantami...
12/05/2026

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa, tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Ali Pantami, na gudanar da ganawa da wasu makusantansa domin duba yiwuwar ficewa daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar adawa ta ADC tsagin Nafiu Bala.

Majiyoyin sun ce wannan mataki na zuwa ne bayan abin da Pantami ya bayyana a matsayin cin amana da rashin mutunta gudunmawar da ya bayar a cikin jam’iyyar APC, musamman dangane da al’amuran siyasar jihar Gombe.

Bincike ya nuna cewa tattaunawar na gudana ne cikin sirri, inda ake nazarin makomar siyasar Pantami da yiwuwar shiga sabon tafarkin siyasa tare da ADC kafin babban zaɓen 2027.

Sai dai har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga Pantami ko shugabannin APC da ta tabbatar da wannan yunkuri.
Me zaku iya cewa?

Dan Allah ku taya mu da sharing zuwa groups...
Sanarwa domin samun ingantattun labarai kuyi Following na:
ANNUR-Hausa
Nigeria Hausa
Madubin Arewa
ALPU Hausa
AGIBASA-Hausa
Madubin Bauchi

DA DUMI-DUMI: Kotu ta soke belin tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, tare da bayar da umarnin kamo shi bayan y...
11/05/2026

DA DUMI-DUMI: Kotu ta soke belin tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, tare da bayar da umarnin kamo shi bayan ya gaza bayyana a gabanta kan shari’ar zargin almundahanar N31bn.

Duk Wanda suke so suyi mulki a qasar nan indai badan su kawo gyara ba Allah ka hanasu kujerar saboda manzon Allah (s.a.w...
11/05/2026

Duk Wanda suke so suyi mulki a qasar nan indai badan su kawo gyara ba Allah ka hanasu kujerar saboda manzon Allah (s.a.w)

Inji Fatima TaBatul

Me zaku ce...

DA DUMI-DUMI: NDC ta hana Kwankwaso yin takara a 2027, Ta ce Dan Kudu ne kawai ke da damar yin takarar shugaban kasa a j...
09/05/2026

DA DUMI-DUMI: NDC ta hana Kwankwaso yin takara a 2027, Ta ce Dan Kudu ne kawai ke da damar yin takarar shugaban kasa a jam’iyyar

Jam'iyyar NDC na gudanar da babban taron ta na kasa a yau Asabar, sai dai a yayin taron, Jam'iyyar ta ayyana cewa ta yanke hukuncin Dan yankin Kudu za ta baiwa takarar shugabancin kasa a 2027 kuma an amince da matakin,

Wannan dai na nufin tsohon Gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ba zai samu damar takara a NDC din ba saboda wannan matsaya da aka cimmawa,

Wace shawara za ku bashi?

Babbar Kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a Kofar Kudu karkashin mai Shari’a Ustaz Ibrahim Sarki Yola, ta yankewa wa...
09/05/2026

Babbar Kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a Kofar Kudu karkashin mai Shari’a Ustaz Ibrahim Sarki Yola, ta yankewa wani limamin Juma’a kuma mai kula da wata makaranta a Abuja, hukuncin ɗaurin wata 1 ba zabin tara, saboda turawa matar aure tsaraicinsa ta WhasApp.

Tun da fari mijin matar ne ya shigar da korafi a wajen yan sanda cewar wanda ake zargin yana neman matarsa tsawon shekara 1.

Limamin ya shafe lokaci yana tura mata tsaraicinsa ta WhatsApp duk da matar ta shaida masa tana da aure amma bai yarda ba.

Ya ci gaba da rokonta da hilatarta cewa ta bashi dama domin yana ganin ba gaskiya bane cewar tana da aure.

Bayan da aka karanta masa tuhumar, limamin ya amsa laifin, har ma ya roƙi kotun ta yi masa sassauci.

Daga bisani mai shari’a Ustaz Ibrahim Sarki Yola, ya yanke masa hukuncin daurin wata 1 ba tare da zabin tara ba.

Ni kam tabbas zomo 9 na gani kaifa?Kuyi following na ANNUR-Hausa
04/05/2026

Ni kam tabbas zomo 9 na gani kaifa?
Kuyi following na ANNUR-Hausa

Kafin yan taadda s**ai masa hari saida s**a gama karantar shige da ficensa, daga ƙarshe s**a gane cewa shi mutum ne da b...
29/04/2026

Kafin yan taadda s**ai masa hari saida s**a gama karantar shige da ficensa, daga ƙarshe s**a gane cewa shi mutum ne da baya wasa da sallar asubahi, yana zuwa masallaci da wuri kullum tun kafin lokacin tayar da salla yayi.

Allah taala ya jiƙan ministan tsaron Mali Sadio wanda yan taada s**a kaiwa hari yana a cikin masallacin dake ajikin gidansa, harin ya rutsa da iyalansa matarsa da yayansa guda biyu, don yan taaddan sun jefa Bom ne a masallaci da kuma gidansa.

Allah ya mana maganin waɗannan yan ta'adan, ya bamu lafiya da zaman lafiya a ƙasashenmu dana musulmi gaba daya.
Me zaku iya cewa?

Address

Alibhausa
Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ANNUR-Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share