23/06/2021
A mulki naga mutuwar Abacha, a sarauta naga ta Sarkin Kano Ado, a basira da azanci naga ta danmasanin Kano, a ilimin addini naga ta Sheikh Jafar da Albani, a dukiya naga mutuwar Sheikh Isiyaka Rabiu da makamantan haka.
Bayan mutuwar su sai naga ba abinda aka fasa. Yadda rana take faduwa a yamma ta fito ta gabas haka take yi. Mutane sun cigaba da harkokin su, matayen su da yayan su ma sun ci gaba da rayuwa ta walwala da jin dadi cikin kankanin lokaci.
Sai na kara tabbatarwa kaina cewa wannan duniyar ba komai bace face mayaudariya kuma duk wanda ya yarda da ita to zata bashi mamaki....
Haka zalika da na ga yadda matan mamata suke rigerigen aure sannan suke kawo mazajen da s**a aura cikin gidajen tsofafin mazajen su su kwanta a kan gadon mamacin da su sannan naga kuma yadda y'ay'a suke rigima akan gadon mahaifan su da yadda suke sharholiya da abinda aka bar musu sannan naga yadda ake fama dasu gurin biyan bashin mamacin, sai na fadawa kaina gaskiya cewa duk wanda ya bari saboda d'a ko mata ko wani ko wata ya sabawa Allah ko ya Tara dukiyar haram, to ya cika cikakken sakarai.
Ita duniyar nan duk girman mutum kuma duk matsayin sa mutuwarsa bata sawa a fasa komai.
Wannan kadai ya ishe ka ishara ka sauke girman kai da isa ka nufi Allah da ayyuka na gari.