04/09/2022
Assalamu Alaikum barkanmu da asubahin Lahadi, bakwai ga watan Safar, shekarar 1444 bayan hijirar cik**akin annabawa kuma fiyayyen halitta, Annabi Muhammad S. A. W. Daidai da huɗu ga watan Satumba, shekarar 2022.
1. Gwamnatin Tarayya ta nanata cewa no work no pay ga malaman jami'a da ke yajin aiki. Wata dai na bakwai ke nan da gwamnati ta dakatar da albashin malaman da ke yajin aikin. Malaman sun ce ba gudu ba ja da baya. Yajin aiki ya ci gaba.
2. Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani rumbun tattara bayanai da adana su, na dukkan wanda wata hukuma ta tsaro ta k**a.
3. Hukumomin 'yan sanda suna nan suna bincikar wani ɗan sanda, da ake zargin ya nemi ya yi lalata da wata budurwa mai shekara 17 da aka tsare ta a ofishin 'yan sanda.
4. Gwamnatin Tarayya, ta ƙara wa ministoci da manyan sakatarori da sauransu, yawan kuɗin alawus na tafiye-tafiye.
5. Hukumomin soja, sun ɓullo da wata horarwa ta soja ta dole ta mako shida, ga yara da s**a kammala makarantar 'ya'yan sojoji da aka fi sani da Military School.
6. Kotu ta wanke tsohon gwamnan jihar Filato Jonah Jang, daga zargin da ake masa na ya wawuri wata Naira Biliyan shida da kusan rabi.
7. A jihar Zamfara masu fashin jama'a sun yi fashin liman da masallata masu yawan gaske a lokacin sallar Jumu'a.
8. A jihar Katsina masu fashin jama'a, sun je rugar fulani, s**a yi fashin fulani da dabbobinsu. Haka nan masu bin jama'a har gida su yi fashinsu sun addabi mutanen Funtuwa.
9. Ƙungiyar Makira Waya ta jihar Kaduna, za ta gudanar da wani babban taronta a Lahadin nan a Kaduna, inda aka gayyaci malamanmu da mu ɗalibai, mu gabatar da maƙaloli. Tawa maƙalar ita ce Dangantar Makira Waya Da Kafofin Watsa Labaru.
10. Ma'aikatan hukumar yaɗa labaru ta jihar Kaduna KSMC, da aka sallama aiki tun wuraren farkon shekarar da ta gabata, ba tare da an biya su abin da ya k**ata a biya su idan za a sallami ma'aikaci rana tsaka ba, suna ci gaba da godon a biya su haƙƙoƙinsu.
Mu wayi gari lafiya.
Af! Ga wata tsintuwar da na yi a fesbuk. Tsintuwa ce kashi ta biyu domin kuwa na taɓa kawo muku kashinta na farko. Ga ta k**ar haka:
'Daga Waziri Aku
ASALIN TAGUWA 2
Kamar yadda na ce idan Allah ya kai mu amaryar wata zan koma ƙauye wurin Kaka Tasalla domin jin tarihin asalin taguwa. To, da ranar ta zo sai na haye babur ɗina na nufin ƙauyen. A kan hanya na ga gonakin da aka noma an fara girbe gero, waɗanda kuma aka bari saura saboda matsalar 'yan ta'adda, duk hambama ta cika su. A nan na gane lallai damina ta tsufa.
Da na isa gidan sai na tarar da matan wan mahaifina a gindin murhu suna gasa tumu, yara kuma sun samo taure a gona suna sha, wasu kuma na shan takanɗa. Na kafe mashin kusa da dabin tumaki, muka g*isa da matan gidan na nufi ɗakin Kaka, na same ta a kan karauni tana taɓa ƙailula. Na yi sallama, ta yi zumut, k**ar wadda aka tsikara da allura, ta tashi zaune tana murje idanu.
Ta dube ni ta ce, "Garbati, kai ne tafe da yamman nan?"
Na ce mata, "I, ni ne Kaka." Na zauna a gefen gado, na fara raba idanu k**ar yadda na saba, ina kallon tarkacen da ke cikin ɗakin. Bayan mun g*isa sai ta jawo gidauniya ta yi mini idon kwaɗi ta ba ni. Na karɓa na shanye. Ita kuma ta ɓalli goro ta jefa baka. Ta kalli kayan da ke jikina ta ce, "ko kai fa ɗan nan, ka ga yau dai ka yi shiga irin tamu ta Hausawa, ba k**ar kwanaki da ka zo da shigar Nasaru ba."
Na ce, "to, da ma zuwa na yi ki faɗa mini tarihin asalin taguwa tun da kin ce ba daga Turawa muka kwaikwaye ta ba."
Ta ce, "af, an kuwa yi haka. Ai na gaya maka tun kan a haifi uwar mai sabulu balbela take da farinta. Ko da Nasaru s**a zo sun iske mu da suturunmu."
Ta zubar da yawu kana ta ci gaba, "Tun can tale-tale Bahaushe bai da wata sutura da ta wuce mayafin saƙi, shi yake ɗaurawa a ƙugu sannan ya yafa shi saman kafaɗa har ya sauka bisa gadon bayansa. Ana kiran wannan shiga da suna lage. To akwai wani mutum wai shi Guwa wanda mayafi ɗaya kurum gare shi, ko datti mayafin nan nasa ya yi, idan zai wanke shi, sai dai ya yi ƙato-gulbi.
Ana nan har mayafin nan ya kai ga hujewa a tsakiyarsa. Da Guwa ya ga haka, ya rasa yadda zai yi, sai wata dabara ta faɗo masa a rai. Ya ƙuga kansa inda mayafin ya huje, sai ko ya ga ya sauka ya rufe masa jiki kaf. Ya samu ɓawon ice ya yi ɗamara don kada iska ya riƙa ɗage shi. Da ya fita waje mutane s**a gan shi, sai s**a yi sha'awar shigar da ya yi. S**a riƙa huje mayafinsu a tsakiya suna cewa bari mu yi ta-Guwa, watau irin dabarar Guwa."
Kaka ta dube ni ta ce, "to ka ji asalin taguwa. Daga bisani kuma aka samu dabarar ɗinke gefe da gefe na mayafin aka daina yin ɗamara. Don haka rigar Bahaushe ta farko ita ce 'yar shara, wacce ake fid da wuya kawai babu hannuwa. Daga nan Nasaru s**a gani su ma s**a kwaikwaya."
Na yi dariya na ce, "ikon Allah, lallai Bahaushe akwai hikima."
Ta riƙe baki ta ce, "kai ɗan nan, me ka ɗauki Bahaushe hala? Ba ka san cewa asalinsa daga Misira yake ba? Ko ba ka san cewa Misira ce tushen ilmi da wayewar kai a duniya ba? Don haka ba abin mamaki ba ne don Bahaushe ya daɗe da wayewa a duniya."
Na ce, "toh, ai ni ban sani ba. Amma wata rana zan so na ji wannan tarihi." Na miƙe tsaye ganin hantsin gwauro ya fara kawo jiki. Muka yi sallama da Kaka, na ba ta na goro na fita. Na bar matan gidan na ɗibar garafuni a jikin damfami, na haye mashin ɗina na nufi gida.
..
Ga ƙarin wasu kalmomin da muke so a gano mana ma'anarsu k**ar yadda s**a fito a cikin labarin:
1. Saura.
2. Hambama.
3. Tumu.
4. Taure.
5. Takanɗa.
6. Dabi.
7. Karauni.
8. Ƙailula.
9. Idon kwaɗi.
10. Ƙato-gulbi.
11. Hantsin gwauro.
12. Garafuni.
13. Damfami.
Bukar Mada
03/09/2022
'
Is'haq Idris Guiɓi
Kaduna Nijeriya