05/01/2021
Wani Jan hankali zan Mana mata, nasan ba kowace zata fahimce ni ba, amma dole zan fada.DAGA ISAH ABOKI NE
Kullum tunanin matan wnn zamanin me zan kara me zan rage a halittar da ubangiji yayi Mana, kullum burin matan yanzu su yi abinda zai birge maza koda hakan nan gaba zai taba lafiyarsu.
Shin su maza Mai suke gyarawa ragewa ko karawa saboda Mace?
Shi namiji halittar sa dole sai ya so mace fiye da 1 haka Allah yayisu, ke dai kiyi kokari ki toshe iya matsayinki a wajensa Amma wlh baki isa duk gyaran da za kiyi ki iya toshe masa sauran wajen ba.
Ku zuba ido da yawan maza lafiyar mace suke mora, da zarar wani Abu ya sameki Mai matukar kirkine zaici gaba da dawainiya da ke, amma fa saiya sake aure, idan jikin yayi tsanani ma a mayar dake gidanki ya dinga zuwa dubiyarki a chan.
Mu farka Mata mu mayarda hankali akan tarbiyyar yara a yanzu, mayar da hankali kacokan da akai akan me zanyi akan wane, shi ya dauke Mana hankali akan Lura da tarbiyyar yara . Idan baki Haifa ba, kanwarki wanki ko yayarki ta Haifa Miki, Dan haka mu gudu tare mu tsira tare.
Bance kar a kula da miji ba kar wasu su min mummunar fahimta.
Allah yasa mu gane.