31/08/2026
MAKARANTAR ALIKO DANGOTE: WATA DAMA DA GWAMNATIN KANO TA YI WATSI DA ITA
Gwamnatin Jihar Kano ce ta samar da Aliko Dangote Ultra-Modern Skills Acquisition Centre, a zamanin mulkin tsohon Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Kudu, Kwanar Gurjiya.
An kashe biliyoyin kuɗi wajen gina wannan makaranta tare da samar da kayan aikin koyo da koyarwa a Ƙaramar Hukumar Dawakin Kudu. Amma abin takaici, saboda rashin kishin al’umma da matasan Jihar Kano, gwamnatin yanzu ta kasa gudanar da ita yadda ya kamata.
Da gwamnati ta damu da makomar ƴaƴan talakawa, wannan makaranta kaɗai za ta iya taimakawa wajen horar da matasa sama da 10,000, ta hanyar koya musu sana’o’i daban-daban tare da ba su jarin fara sana’ar da s**a koya, domin su dogara da kansu.
Saboda wannan gazawa, sai aka bai wa Dangote Foundation makarantar bisa yarjejeniyar shekaru 20. Alhali makarantar ta shafe sama da shekaru biyu a rufe ba tare da gudanar da ayyukanta yadda ya kamata ba. Kayan aikin da aka zuba a cikinta sun yi ƙura; sai mutum ya je ya ga irin kayayyakin da aka tanada sannan zai fahimci irin aikin da gwamnatin Dr. Abdullahi Umar Ganduje ta yi. Ko ba ka son Ganduje, dole ne ka yaba masa a kan wannan aiki.
Abin takaici ne matuƙa yadda wata babbar makaranta mai irin wannan muhimmanci, wadda jihohin maƙwabta za su yi fatan samun irinta, za a bar ta tsawon lokaci har ta fara fuskantar lalacewa saboda rashin kulawa.
Insha Allah, idan Comrd. Aminu Abdussalam Gwarzo ya zo, za mu tabbatar mun ba shi shawarar a dawo da wannan makaranta ƙarƙashin kulawar Gwamnatin Jihar Kano, domin ta ci gaba da amfanar ƴaƴan talakawa. Domin na san shi da kishi da son ganin ɗan talaka ya amfana.
A cikin yarjejeniyar da za mu mara masa baya a kanta, wajibi ne ya fifita buƙatar talakawa a kan tasa, kamar yadda muka sanya buƙatar talakawa a gaba kafin tamu.
Insha Allah, muna da kyakkyawan zato cewa za mu ga sabuwar Kano ƙarƙashin jagorancin Comrd. Aminu Abdussalam Gwarzo a 2027, Kano da za ta bambanta da yadda take a yau — domin abin da muke gani a yau abin takaici ne.
Zaɓen 2027 zaɓe ne na cancanta, ba maganar jam’iyya kawai ba. Duk inda ɗan takara na ƙwarai yake, ku zaɓe shi.