Muryar Negriar hausa

Muryar Negriar hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Muryar Negriar hausa, Business service, Hotoro, Kano.

08/08/2023
02/08/2023

Ina zasu fito su magana akan tallafin man fetur, bayan ana ciyar dasu da dukiyar talaka, suna sha daga ita, suna hawa motocin alfarma, suna auren mata masu daraja, suna daukar nauyin karatu da rayuwar ƴaƴansu cikin alfahari da jin dadi.

A lokacin da abinda talaka zaice sau daya a rana wuya yake masa, bai iya rike aurensa b***e ya kula da yayansa, yaran 'yan mata suna kara zama karuwan waɗancan 'yan boko da 'yan siyasa masu rike da madafun iko.

Matasa kuma na kara zama yan bangar siyasar su da masu yi musu yakin neman zabe, su kuma suna saka musu da kudin siyan kwayoyi da makaman da zasu dinga kisan junansu da addabar Al'umma da su.

Idan baka san wacce kasace mai mulkinta ya maida wanda yake Mulka bayi ba, kazo Nigeria kayi kallo, yau an wayi gari babu wani bangare na rayuwa dake da sauki a wannan kasa, wai kasar da wutar lantarki babu, lafiya, tsaro, komai a lalace yake wai sune suke cire tallafin man fetur.

Inna lillahi wa inna ilaihirraji'un, Allah kayi mana maganin waɗan nan azzalumai.

Árdá Gụ́lèryasanya Riga Mai lamba 24No.Waishin Wannan Yaron Musulmi ne ko Christer?
07/07/2023

Árdá Gụ́lèr
yasanya Riga Mai lamba 24No.
Waishin Wannan Yaron Musulmi ne ko Christer?

Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da karin kudin kira ga kamfanonin sadarwa na 5%. Sannan an rage haraji kan wasu motoci da...
07/07/2023

Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da karin kudin kira ga kamfanonin sadarwa na 5%. Sannan an rage haraji kan wasu motoci da ake shigowa da su kasar.

Ya kuka ji da wannan mataki na shugaban kasa?

30/05/2023

Assalamualaikum

Jiya Nayi magana akan maza masu taɓa Mata kowacce kmr tana jira, ji kake ana Juu faɗa musu dai 😒

Ja'ira yau kanki na dawo Algunguma 😒🤌 idn akazo case irin wannan gaskiya bana ganin laifin Namijin sosai, Saboda duk abinda zai faru acikin barna irin wannan laifin mace yafi yawa.

1. Na farko wasu matan su suke Fara taɓa mazan ma dakansu ko Kuma su bada fuskar da za'a taɓa su idn namiji baiga fuska ba Wlhy duk girmansa ko yawan shekarunsa babu yadda ma za'ayi har ya Fara kokarin taɓa ki,,,karyansa ne Wlhy

2. Na biyu Yana da alaqa da yanayin shigar da k**eyi

3. Na uku Yana da alaqa da yanayin da k**e Masa magana as in idn kuna ganin Juna Kuma kina Yi Masa magana cikin shagwaba wlhy ko shi ne allon da ake liqawa a masallaci wataran sai kin saka shi ya kauce hanya,,, so ba'a Hana ki Masa shagwaba ba Amma kisan wace iri zakiyi Kuma a Ina ? E get why🤷‍♀️

4. Na Huɗu Yana da alaqa da yawan son da k**e Masa Wanda yake Hana ku faɗawa juna gaskiyar cewa wannan abinda muke fa bashida kyau ya Sabawa koyarwar musulunci..... So zaka ga yawancin Mata idn muna masifar son saurayi mukan Bari shaidan yayi galaba akanmu muga kmr soyayya ce.

5. Na Biyar wasu sun dauki hakan wayewa ce,,, idn ma namijin baya kokarin taɓa su gani suke Yi baya sonsu akwai wacce Yake so Kuma yake taɓawa kaico 🥹 so gaskiya mostly nafi ɗora blame akan Mata idn akazo magana irin wannan,,, sbd wlhy namiji Bai Isa ya Miki Dole ba matuqar ba mijinki bane,,, ko me zai faru sai idn kece kika yarda.....
Ban cire kaina ba Kuma ban cire kowa ba...., domin kowani bawa akwai laifin daya boye a ransa kasancewar mu Ya'yam Adam Dole akwai ajizanci,,,,Ina Mana nasihar muji tsoron Allah,,, acikin maza idn kasan halinka ne taɓa yaran mutane kaji tsoran Allah kadaina Dan uwa😢 kema idn kin San kina sakar Masa jiki Yana shafaki kiji tsoran Allah kidaina....Mudaina barin so Yana rufe Mana idanuwa muna aikata sabon Allah🙏🏻

Babu amfanin soyayyar da baza'a tunatar da juna faɗin Allah ba 💔 Mu tsaftace so

Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari Ya Sauka A Mahaifarsa Daura Dake Jihar Katsina.
30/05/2023

Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari Ya Sauka A Mahaifarsa Daura Dake Jihar Katsina.

Media Services LTD

30/05/2023

An rantsar da Abba kabir Yusuf a matsayin Gwamnan Jihar kano

BABBAN TASHIN HANKALI!!!Hadisi ne zan karanta muku Amma ina neman alfarma guda awajenku kafin ku karanta Hadisin nan... ...
13/05/2023

BABBAN TASHIN HANKALI!!!

Hadisi ne zan karanta muku Amma ina neman alfarma guda awajenku kafin ku karanta Hadisin nan... Alfarmar da nake nema awajenku ita ce, ku tsayar da duk abinda kukeyi, ku nutsu ku karantashi da kyau.

Domin na tabbata sai ya girgiza zuciyar duk wani mai Imani.

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM.
Tsira da aminci su tabbata bisa Annabin Karshe, da dukkan Iyalansa da Sahabbai baki daya.

Yazeedur Raqqaashiy ya karbo Hadisin daga Anas bn Malik (R.A) yana cewa:
Watarana Mala'ika Jibreelu (A.S) yazo wajen Manzon Allah (S.A.W) awani lokacin da bai saba zuwa masa ba.

Yazo, gaba dayan launin fuskarsa
ya canza. Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa "MAI YASA NAGA LAUNIN FUSKARKA DUK YA CANJA HAKA?".
Yace "Ya Muhammadu (S.A.W) nazo maka ne awannan lokacin da Allah yayi Umurni da Masu hura wuta suci gaba da Hura ta.

Duk wanda yasan cewa Jahannama gaskiya ce, Wuta gaskiya ce, Azabar Kabari gaskiya ce, kuma Azabar Allah ita ce mafi girma, to bai kamata yayi wani farin ciki ba har sai ya tabbatar da cewa ya samu tsira daga wannan".

Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa "YA JUBREELU INA SO KA SIFFANTA MUN YADDA JAHANNAMA TAKE".

Sai yace "Na'am. Hakika Allah madau kakin Sarki yayin da ya halicci Jahannama, yasa an hurata tsawon Shekaru DUBU. Har sai da ta zama JA -JAWUR.

Sannan aka sake hurata tsawon Shekaru DUBU har sai da ta zama FARI - FAT!!
Sannan aka sake hurata tsawon shekaru DUBU har sai da ta zama BAKA - KIRIN!!!.
Tana nan har yanzu BAKA KIRIN ce, mai
tsananin duhu ce.Harshen Balbalinta basu mutuwa ballantana Garwashinta.

Na rantse da Girman Ubangijin da ya aikoka da gaskiya, da ace za'a bude misalin kofar allura daga wutar Jahannama, Wallahi sai dukkan Ma'abotan doron duniyar nan sun kone baki dayansu saboda tsananin zafinta.
Na rantse da girman Ubangijin da ya aikoka da gaskiya, da ace za'a ratayo tufafi guda daya tufafin 'Yan Wutar Jahannama a makaloshi atsakanin Sararin Samaniya, da sai Dukkan Ma'abotan doron kasa sun Mutu baki dayansu saboda tsananin

Address

Hotoro
Kano

Telephone

+2349033063541

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Negriar hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share