03/01/2026
MUTANEN JIHAR BAUCHI SUN NUNA BACIN RANSU KAN YUNKURIN BATA SUNAN GWAMNANSU
Hakika, kowane mutum yana da abin yabo da kuma abin kushewa, domin gaskiya ta fi Ζarfin kowa. A fagen siyasa kuwa, an san cewa ana amfani da kowace dama da kowanne salo domin cimma buri, musamman idan aka samu wata kafa ta aiwatar da hakan ta kowace hanya.
Ba wai muna neman yin sharhi ne domin karyata binciken da Hukumar EFCC ke yi ba, domin bincike hakki ne na doka, kuma babu wanda ya isa hana aiwatar da shi. Sai dai muna magana ne bisa abubuwan da s**a bayyana a zahiri, musamman game da gudunmawar Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed wajen inganta tsaro da zaman lafiya a Jihar Bauchi.
Ko wanda bai yarda da siyasar gwamnan ba, ba zai musanta irin ΖoΖarin da ya yi wajen dakile ayyukan taβaddanci da tabbatar da tsaro a jihar ba. A tsawon lokacin da ya shafe yana mulki, alβummar Jihar Bauchi sun shaida matakan da ya Ιauka a fili, tare da cikakken haΙin gwiwa da dukkan hukumomin tsaro.
Mutum ne da tarihin rayuwarsa ya ginu kan girmama doka da bin Ζaβida, wanda ba a taΙa jingina masa da laifuka makamantan waΙannan ba tsawon tarihinsa. Saboda haka, alβummar da s**a rayu da shi suna kallon wannan batu a matsayin yunkurin siyasa, ba gaskiyar alβamari ba.
Haka kuma, tuhumar da ake alakanta wa EFCC ta kasa jingina gwamnan da ayyana ko tallafa wa wata Ζungiyar taβaddanci guda Ιaya kai tsaye. Sai dai an takaita zargin da kiran sunaye ba tare da hujjoji bayyanannu ba, abin da ya sa hankalin masu tunani bai kwanta da wannan zargi kwata-kwata.
Muna jin takaici da haushin yadda ake ΖoΖarin juya lamarin bincike zuwa makamin siyasa, domin bata sunan jihar mu da kuma gwamnan muβmutum mai daraja da mutunci a idon doka, kuma abin alfahari ga alβummarsa.
Muna kira ga masu ruwa da tsaki da su duba kimar Jihar Bauchi, wadda ta zama mafaka ga alβummar shiyyar Arewa maso Gabas, sakamakon ingantaccen tsaro da gwamnatin jihar ta samar. Duk mai kishin Ζasa zai yi shakku matuΖa wajen jingina gwamna mai irin wannan ΖoΖar