Yan uwa meye mafita?

Yan uwa meye mafita? Mun buda wannan Shafin ne domin neman shawara da kuma bada ta komai dacin ta akan wannan gwagwarmaya

23/02/2026
DA DUMI-DUMINSAA UNGUWAR ZABI DAKE ZARIYA DILLALAI SUN HAƊA BAKI DA MASU GARI SUNA AUNE FILAYEN DAKE KAN BUTUTUN MAI SUN...
03/09/2024

DA DUMI-DUMINSA

A UNGUWAR ZABI DAKE ZARIYA DILLALAI SUN HAƊA BAKI DA MASU GARI SUNA AUNE FILAYEN DAKE KAN BUTUTUN MAI SUNA SAYARWA.

DON HAKA NAKE SANAR DA HUKUMAR DA KE KULA DA WANNAN BUTUTUN MAI DA SU GAGGAUTA ZUWA WAJEN DON SU GANI DA IDON SU SU DAUKI MATAKIN DAKATARDA WANNAN SHIRIN.

DOMIN DUK WANDA AKA SAYARWA WADANNAN FILAYEN BA SHAKKA AN ZALUNCE SU.

DAGA MAJIYA MAI TUSHE

MAI TABBATAR DA GASKIYAR LAMARIN YA TUNTUBI WANNAN NUMBER

07015126612

Don Allah Jama'ah yada mana wannan labarin wallahi gaskiya n

Alhamdu Lillah mai son tambaya ko amsa ko mukabala akan addinin musulunci na kowane mangare Sunnah ko Shia ko darikun su...
13/10/2023

Alhamdu Lillah

mai son tambaya ko amsa ko mukabala akan addinin musulunci na kowane mangare Sunnah ko Shia ko darikun sufaye

to ga wani group da muka buda na WhatsApp sai dai akwai kaidoji dokoki kamar haka

ba'a cin mutuncin malamin wani ko zagin wani ko saka vedio ko hoto sai in hujja zaka kafa akan su idan kuna bukatar shiga gashi nan

WhatsApp Group Invite

YAKAMATA AYIWA LAUYA DAN BAITO TINI ,YANASO YABATAWA KOTU LOKACI, KAN BATUNSA NA SUNDUBA MUSLIMU BASU GANIBA , YAKOMA YA...
10/06/2022

YAKAMATA AYIWA LAUYA DAN BAITO TINI ,YANASO YABATAWA KOTU LOKACI, KAN BATUNSA NA SUNDUBA MUSLIMU BASU GANIBA , YAKOMA YADUNA ZAMAN KOTU NA RANAR

CIKAKKEN RAHOTON ZAMAN KOTU NA RANAR 3/3/2022

Da farko an samu tunja-tunja akan barin masu taimakawa malam su shigo domin mika masa littattafai daga karshe Malam yace babu komai zai yi da kansa.

Alkali: Zaka dauki alkawarine ko kuwa zaka rantse da Alqurani?

Malam: Zan rantse kuma ina da alwala nan take kotu ta rantsar dashi.

Malam: Na farko acikin tuhumar farko akwai kusakurai da yawa tun daga ranar da s**ace nayi wannan karatu wato karatu na 93, to ba a wannan ranar nayi shiba. Na biyu Cewar sun duba basu ga wannan lafazi ba ya nuna cewa sun gini tuhumarsu akan dayan abu biyu.

Kodai rashin sani ko take sani wanda a ka’idar malaman hadisi idan akace wane yayi ruwaya to ba lafazi kadai ake nufiba, takan yiwu lafazine kamar yadda takan yiwu ma’anar lafazine amma ba lafazin ba don haka idan mutum yace anyi ruwaya to ka’ida sai a fara dubawa aga lafazi yake nufi ko ma’anar lafazi idan an duba ba lafazi aka samu ma’ana to ruwaya ta tabbata kuma na Dogara da abinda yake cikin littattafan hadisi ina neman bujurar dasu.

Alkali: Kotu ta baka damar yin haka.

Malam: Na farko “Al muhaddisul fasil bainar rawiy wal wa’iy” na Ramahurmuziy. Shafi na 551 yayi babi mai taken “Man kala bi isbatul ma’ana” Daga Hassanul basari yace Iza asabta ma’anal hadisi ajza’aka. Ma’ana idan ka dace da ma’anar hadisi to yin hakan ya wadatar. Abi Hamza ya cewa Ibrahimu nakha’I, muna jin hadisi daga gurinka amma bama samun damar mayar dashi irin yadda mukaji daga gareka sai yace masa shin idan ka saurara kana iya gane halak daga haram yace, eh sai yace ai haka muma muke zantar da hadisi.

Ibn sirina yace da yawa muna jin hadisai daga mutum goma amma kowanne lafazinsa daban. Yahaya bn Adam yace naji Safiyanussauri yana cewa “ Mu muna zantar daku hadisi da Ma’ana”. Sha’abiy yace, na cewa Ibn Abbas ka kasance kana zantar damu hadisi yau sannan gobe kuma sai ka cudanya shi sai Ibn Abbas yace masa a halin yana cikin fushi shin bazaku yarda ba da ku haddace Ma’anar hadisi.

Daga cikin babin bayanin kan malaman da s**a iyar da hadisi da Ma’ana ba lafazi a duba shafi na 89, 315,16,17 duk sun ce idan dai an fadi ma’ana ba sai an kawo lafaziba.

Na biyu: Abu amrin Kurdabiy a cikin Littafinsa “Jami’u bayanil ilmi wa fadlihi” shafi na 111 yayi babi mai taken “Al amru bi islahil lahni wal khada’I fil hadisi wa tatbu’ul alfaaz” wato babi kan “Umarni da gyatta kuskure da bibiyar lafazan hadisi da ma’anoninsa” Anan Malam yayi Karin bayani akan yin hadisi da ma’ana a shafi na 359, da 360. Kuma akwai wata maganar ta Abuldarda’I a shafi na 361, kuma ibn sirin ya kawo wata maganar a 365, 366 daga hasanul basari da take tabbatar da haka sannan ya kuma ya kawo maganar imamu Malik a shafi 113 daga ibn Abdul barr daga Imamu Malik yace na tambayi Malik kan yanayin zantar da hadisi Maliku yace idan dai maganar Annabi ce ina kin bayani da Ma’ana, amma ta waninsa babu laifi. Ashhabu ya tambayi Maliku yace idan a hadisi ne ake samun karin harafi ko ragi amma ba Ma’ana bata canjaba. Sai yace a wannan abune sassauka.

Na Uku: “ Al kifaya fi ma’arifati usulu ilmir riwaya”. Muzalladi na 1 dana 2 shafi na 558 Shima duk wadannan maganganun yayi tun daga shafi na 558 haka a mujalladi na biyu har zuwa shafi na 27 wadannan maganganune harma da kari na ruwaya da ma’ana ba da lafaziba.

Na hudu: “Mu’ujamus sahaba” juzu’I na biyu shafi na 215 na ibn Amr Tarjamar Abdullahi Muhammad bn sulaiman bn Ukaimatil laysi tarjama ta 518.
Anan ne malam ya koro ruwaya daga Khadibul bagadadiy yace ana tambayi ma’aikin Allah cewa mu munajin hadisi kuma mu kasa zantar dashi yadda ka fada sai shugaba (S.A.W.) yace idan baku halatta haramba kuma baku haramta halal babu laifi.

Na biyar: “ Aljami’u li akhlaqir rawiy wa adabus sima’I” juzu’I na biyu shafi 78 babi mai bayani akan wadanda s**a tafi akan zantar da hadisi da ma’ana ya kawo maganganun malamai ya lissafo tabi’ai da malamai da suke kan haka.

Littafi na shida: “Tanqihul anzaar” na ibn waazir Al yamani juzu’I na biyu shafi na 363’

Littafi na bakwai: “ Tauhidul afkar” juzu’I na biyu shafi na 363 na Amirul san’aniy, yana cewa halalne yin ruwaya da ma’ana da haduwar malamai akan haka har yace an halarta yin ruwaya da wani yare.

Littafi na takwas: “ Al tabsira fi usulul faqh” na Abu ishaqa ibrahima bn Ali ( Fiiruu-zaa badiy) ya kawo malaman da suke musa yin haka kuma yayi musu raddi a ciki yace idan ma’ana tayi daidai to babu laifi.

Littafi na tara: “irshadul fuhul ila tanqihul haqqi min ulumil usul” na shaukaniy acikin shafi na 221 a karkashin fasalin da yake bayanin halaccin ruwaitar da hadisi da ma’ana.

Littafi na goma: “ An nukatu ala miqaddimatu bn rusdin” juzu’I na biyu shafi na 68 Mas’ala ta 401 a cikin babi mai suna idan mai hadisi zai zantar dashi ba da lafazi ba da ma’ana. Sannan Mas’ala ta bakwai shafi na 612 yace ya halarta takaice hadisi a fadi ma’anar kuma ace anyi ruwaya kamar yadda nayi s**ace sun duba basuga lafazin ba.

Adaidai wannan gabane Alkali ya tafi hutun minti talatin.

Bayan dawowar sane daga hutu malam yayi yunkurin ci gaba da dakko sauran littatafan da s**a rage sai Alkali yace KO ZAKA BAR SAURAN AI WANNA MA SUN ISA HUJJA DOMIN IDAN MUTUM A JARRABAWA YA KAFA HUJJA DA LITATTAFAI GOMA SHA DAYA AI YACI JARRABAWA.

Malam: Bayan duk abin da ya gabata ina da hujjata da na Dogara da ita ta ginar wadannan litattafai guda ashirin da bakwai amma inaso na rufe wannan gaba da littafi mai suna “Algaya” sharhin mazzumatul gaya ta Shamsuddenil Assakhawiy shafi na 51 baiti na 66,67,68, fasali mai suna “Arruwaya” Ibnl jazari yace shin ya inganta na kawo hadisi da ma’ana ba da lafazi ba yace zaka iya ga wanda yasan ma’anar tayi daidai da lafazin tsakanin wanda yake karanta isnadi a ruwaya Amma wanda ya yake karatu ga jama’a yake kafa hujja da hadisi wannan ba sabani kan halarcin yin hakan shi ne ni kuma abinda nayi a wannnan karan dunkule hadisai guda biyu wadanda s**a bada ma’anar hadisai 15 to hade sun da nayi na bada ma’anar a dunkule gata a baiti na 69 shafi 52 yace ya halarta a hade hadisai a bada ma’anarsa a dunkule yin hakan ya halarta kai tsaye.

Dahawiy yace bukhari yana hade hadisai ya fitar da ma’ana kuma ya tsitsinka hadisi.

TA'ADDANCIN NURA HAUSARE A JIHAR SAKKWATO.Nura Hausare wani tsohon Area Boys ne da ya ke amfani da addini wurin aikata a...
11/05/2022

TA'ADDANCIN NURA HAUSARE A JIHAR SAKKWATO.

Nura Hausare wani tsohon Area Boys ne da ya ke amfani da addini wurin aikata ayyukan ta'addanci a cikin al'umma. Mutum ne da babu mutunci ballantana ragowa a cikin mu'amalarsa da mutane. Bushewar zuciyarsa ta yi sanadiyyar 'kauracewar Imani, Kunya da kuma tsoron Allah daga cikinta.

Ko bayan kasancewarsa gogaggen ma'karyaci, mayaudari kuma makirin Allah, haka kuma ya na daga cikin mutanen nan da su ke amfani da kalmomin "Shi'a" "Sunnah" "Son Annabi" "Baraden Sunnah" a matsayin makaman da ya ke ya'kar duk wanda su ka samu sa6ani da shi. Wallahi ko ku'di Nura Hausare ya nema a wurinka, idan ka hana shi, kawai zai jefe ka da 'dayan daga cikin alkalmomin nan da na ambata.

Mafi yawan lokota ana amfani da shi ne a matsayin "Karen Farautar 'Yan siyasa" domin cimma burinsu a siyasance. Ya jagoranci kisan mutane fiye 40 a nan cikin jihar Sakkwato. An sassare wasu da adduna, an yiwa wasu yankan Rago a gaban iyalansu, an rusa gidaje tare da sace dukiyoyin al'umma da umurninsa.

Duk matasan da ya yaudara a wancan lokaci, ya h**e musu kunne, ta hanyar zuga su tare da yi musu kirari gami da sanya musu suna "Baraden Sunnah" yanzu duk sun nakkasa, sun wula'kanta, da yawa daga cikinsu an kasheshu kashin 'kas'kanci, wasu kuma son koma musakai!

Ya Allah Ka isarma wa'dannan matasan da Nura Hausare ya lalatawa rayuwa. Ya Allah Ka sakawa iyayen yaran da Nura Hausare ya kassara rayuwar 'ya'yansu.

30/09/2021

A SHIRYE NAKE NA SAKE SHI YA TAFI IN HAR HUJJAR DA ZASU GABATAR BATA DA KARFI KODA KUWA BAKU NEMA BA.

Hakikar Abunda ya gudana a kotu a yau Alhamis 30/09/2021:

Bayan gabatar da sababbin lauyoyin da suke wakiltar Maulana Amirul wa'izina wanda Barister Umar Muhammad yake jagorantar su Abubuwa kamar haka sun gudana:

1-Barister Umar Muhammad ya nemi belin Malam.

Sai lauyan gwamnati Sa'ida SAN yayi s**a akan hakan

Sannan Alqali yace:

bazan baku belinsa ba a yanzu saboda yayi huri kodan tsare rayuwarsa yadda yake da masoya masu yawa haka yake da magauta masu yawa kuma yana da saɓani dasu yayi gabas sunyi yamma.

Amma idan s**a gabatar da shaidun su naga basu da wani karfi zan sake shi ya tafi ko baku nema ba.

2- Lauyan Malam ya nemi a bashi kwafin shari'ar dan yasan daga inda aka fito da kuma inda ake a yanzu.

3-lauyan malam ya fadawa Alqali cewa:

Naji labarin a zaman da ya gabata kace za ka bawa malamin cikakkiyar dama na yazo da dukkan abunda yake so da zai bashi damar kare kansa da kuma cikakken lokaci na gabatar da bayanan sa, ya me girma me shari'a ina son sanin gaskiyar wannan labari.

Alqali:

Tabbas na faɗi hakan kuma kotu bata baki biyu hasali ba Alfarmace za muyi masa ba dole ne ma muyi masa hakan dan doka ce ta bashi damar amma yanzu ba azo wannan gaɓar ba tukunna idan lokacin yayi zaizo da duk abubuwan da zai bukata dan kare kansa, litattafan sa in sunkai cikin mota yazo dasu zamu bashi dama da isasshen lokaci.

4-Barista Umar ya bukaci lauyoyin gwamnati zama na gaba su fara gabatar da shaidun su dan shari'a ta tura kada a cigaba da ɓatawa kotu lokaci.

Inda lauya Sa'ida SAN yace su dama suna zuwa da shaidun su gaban kotu rashin basu damar gabatar dasu shi yasa basu gabatar ba.

Anan Alqali ya amince da suzo su gabatarwa da kotu shaidun nasu a zama na gaba sai dai shaidu 2 kawai yake nema.

Daga nan mai shari'a ya dage Shari'ar zuwa sati biyu masu zuwa ranar 14/10/2021.

Muna Rokon Allah ya kara dora gaskiya a saman karya yayi riko da hannun me shari'ar zuwa ga gudanar da Adalci.

28/09/2021

Jami'an tsaro sun afka ma yan Shi'a masu zanga zangar lumana a Abuja har sun kashe mutane da dama

Allah ya kawo mana zaman lafiya a duniya baki daya

Address

Kaduna
Zaria

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yan uwa meye mafita? posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share