ADN Media Networks Ltd.

ADN Media Networks Ltd. Shafin Kawo Taikatatun Labarai Na Cikin Gida Da Waje, Bayyana Ra'ayi A Fannin Siyasa, Tallata Kayan Kasuwanci, Nishadantarwa Ilimantarwa, kimiyya da Fasaha .

Dahir Abdurrahim consultancy services limited provides a wide range of services to businesses and organizations, including but not limited to business planning, project management, marketing, public relations and Agricultural products. The company also offers technical assistance and support in a variety of fields, including information technology, engineering, and environmental management.

19/08/2026

"Ana zagina baya damuna, amma ina da Mahaifiya tayar mata hankali da mutane su ke yi shi yafi damuna" - Hadiza Gabon

19/08/2026

Bala Muhammed Gwaman Jahar bauchi.

'Yan sanda da sojoji sun tare tsoffin sojojin NajeriyaJami'an tsaro sun hana wasu tsoffin sojojin Najeriya (Ex-serviceme...
19/08/2026

'Yan sanda da sojoji sun tare tsoffin sojojin Najeriya

Jami'an tsaro sun hana wasu tsoffin sojojin Najeriya (Ex-servicemen) gudanar da zanga-zanga a harabar Ma'aikatar Tsaro da ke Abuja.

Tsoffin sojojin sun taru ne domin neman a biya musu wasu haƙƙoƙin fansho da gyare-gyaren fansho da suke cewa gwamnati na binsu.

Sai dai 'yan sanda da sojoji sun tare su tare da hana su shiga harabar ma'aikatar, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce.

📷 Punch

19/08/2026

Yadda Ministan Ayyuka, Injiniya David Umahi, Yaci Gyaran Injiniyoyi Turawa Akan Hakikanin Yadda Aikin Wata Babbar Hanya Zai Kasance.

Hukumar kula da kayayyakin kasuwanci FCCPC tana bukatan sanin dalilin da ya sa buhun siminti ya kai N15,000 a Nijeriya.
19/08/2026

Hukumar kula da kayayyakin kasuwanci FCCPC tana bukatan sanin dalilin da ya sa buhun siminti ya kai N15,000 a Nijeriya.

Jami'ar jihar Kaduna KASU ta Karyata Ikirarin ASUU Na Cewa Malamai 200 Sun Yi Murabus.Mataimakin Shugaban Jami’ar Jihar ...
18/08/2026

Jami'ar jihar Kaduna KASU ta Karyata Ikirarin ASUU Na Cewa Malamai 200 Sun Yi Murabus.

Mataimakin Shugaban Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), Prof. Abdullahi Ibrahim Musa, ya musanta ikirarin ASUU-KASU na cewa malamai 200 sun yi murabus daga jami’ar saboda rashin kyawun yanayin aiki.

VC ɗin ya ce wannan ikirari ba shi da tushe a bayanan jami’ar, yana mai cewa sauyin ma’aikata sakamakon murabus, ritaya, sauyin aiki ko neman wasu damar sana’a abu ne da ya saba faruwa a jami’o’i.

Ya kalubalanci ASUU da ta gabatar da hujjoji masu inganci, ciki har da sunayen malaman da ake cewa sun yi murabus, ranar da s**a yi murabus da kuma dalilan barin jami’ar.

Prof. Musa ya bayyana cewa gwamnatin Gwamna Uba Sani ta kashe sama da ₦800m wajen jin daɗin ma’aikata cikin shekaru uku, sannan ta biya ₦146m na albashin da aka riƙe da wasu alawus-alawus da aka gada daga tsoffin gwamnatoci.

Ya kuma ce an kafa tsarin tallafin ₦50m duk wata tsakanin gwamnatin jihar, shugabancin jami’a da ASUU-KASU domin tallafa wa jami’ar.

A shekarar 2026 kaɗai, gwamnatin jihar ta kuma fitar da sama da ₦200m don gudanar da ayyukan jami’ar, yayin da sama da ₦300m aka zuba wajen tantancewa da sabunta akrediteshin na shirye-shiryen karatu.

VC ɗin ya ƙara bayyana cewa KASU ta kafa cibiyoyin bincike 14 da cibiyoyi na musamman guda biyu, tare da samun tallafin bincike na ƙasa da ƙasa guda bakwai cikin shekaru uku.

Ya ce jami’ar ta kuma samu ₦1bn TETFund domin aikin noma na kasuwanci, yayin da rage kuɗin makaranta da gwamnatin Uba Sani ta yi a jami’o’in jihar ya taimaka wajen rage wa iyaye da ɗalibai nauyin kashe kuɗi.

Prof. Musa ya amince cewa har yanzu akwai wasu matsalolin jin daɗin ma’aikata da ba a warware su ba, amma ya ce gwamnati da jami’a na ci gaba da magance su.

Ya roƙi ASUU-KASU da ta guji duk wani mataki da zai kawo cikas ga karatun ɗalibai, yana mai jaddada cewa tattaunawa da fahimtar juna ne hanya mafi dacewa wajen warware matsalolin ma’aikata, yayin da yajin aiki ya kamata ya zama matakin ƙarshe.

Yanzu dai tambayar ita ce: Shin ASUU za ta fito da sunayen malaman 200 da ta ce sun yi murabus, ko kuma za a ci gaba da musayar zarge-zarge tsakanin ɓangarorin biyu?

Basu wuce malamai 50 ba, da s**a ajiye aiki a jami'ar jahar kaduna ba KASU. ~Inji gwamna Senator Uba Sani
18/08/2026

Basu wuce malamai 50 ba, da s**a ajiye aiki a jami'ar jahar kaduna ba KASU. ~Inji gwamna Senator Uba Sani

18/08/2026

Duk manyan masu kuɗi ko mulki da s**a yi gine-gine a kan magudanan ruwa wanda ke haddasa ambaliya a duk shekara tsawon shekaru, amma aka kasa ɗaukar wani mataki a kansu.

“babu shakka sai an rushe duk wani ginin da aka yi a kan hanyar ruwa, kamar yadda yake a cikin tsarin gina Birnin Tarayya (Abuja Master Plan).”

— Nyesom Wike.

Shugaban ASUU reshen jami'ar, ya bayyana cewa an cimma yarjejeniyoyi tsakanin gwamnati da ƙungiyar ''amma har yanzu jami...
18/08/2026

Shugaban ASUU reshen jami'ar, ya bayyana cewa an cimma yarjejeniyoyi tsakanin gwamnati da ƙungiyar ''amma har yanzu jami'ar jihar Kaduna ba a fara amfana ba''. A cewar sa hirarsa da BBC Hausa

Kamfanin Matatar Man Fetur na Dangote ya sami kwangilar dala biliyan 1, gami da wani kamfani mai zaman kansa na dala mil...
18/08/2026

Kamfanin Matatar Man Fetur na Dangote ya sami kwangilar dala biliyan 1, gami da wani kamfani mai zaman kansa na dala miliyan 600, kafin IPO da aka tsara.

Address

Sabon Gari Zaria
Abuja

Telephone

+2348101465449

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ADN Media Networks Ltd. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ADN Media Networks Ltd.:

Shortcuts

Share