Mujahid Saleh Saad - Dan maliki

Mujahid Saleh Saad - Dan maliki E-Businesses nationwide we deal with business and services

Abubuwan da ake bukata wajen tantantace yan Sanda wanda zaa fara yi 8 ga watan January 2024.(1) sabon hotonka na passpor...
04/01/2024

Abubuwan da ake bukata wajen tantantace yan Sanda wanda zaa fara yi 8 ga watan January 2024.

(1) sabon hotonka na passport.
(2) takardan shaidan lafiya daga asibiti.
(3) takardan shaida na tabbacin halayya daga Mai anguwa ko kuma basarake a kauyenku.
(4) takardan indigin, tare da sa hannun chiyaman dinku na LGA.
(5) Katin shaidar Dan kasa NIN [NIMC].
(6) takardan jarabawar Neco/Waec, takardan haihu [certificate of birth/ takardan shekaru [declaration of birth].
(7) takardan form din da ka cika na police.
(8) Guarantors form wanda duk sun saka hannu a cikin takardan.
(9) takardan gayyantan jarabawa [invitations slip].

Note: Duk wani wanda be zo da wadannan takardun ba, zai iya samun matsala wajen tantancewar da zaa fara na yan Sanda a ranar 8 ga watan January 2024.

Allah ya bada saa

Digirin Sati 6 a Cotonou, Benin Harda zuwa bautar Kasa [NYSC].Wannan da kuke gani shine Umar Audu Saleh, Maaikacin gidan...
30/12/2023

Digirin Sati 6 a Cotonou, Benin Harda zuwa bautar Kasa [NYSC].

Wannan da kuke gani shine Umar Audu Saleh, Maaikacin gidan jaridar Daily Nigeria.

Malam Umar Saleh yayi binciken diddigi inda ya tabbatar da kammale Digiri a sati 6 kuma har yaje bautan kasa wato NYSC.

A shekarar 2022, Dan jaridar Umar Audu ya fara binciken yanda ake siyar da digirin kasar benin, wanda aka hada shi da wanda ya kware a harkan saye da siyarwa na kwalayen Digiri din.

Umar ya tabbatar wa gidan jaridar sa cewa digirin din ya kaso kan farashi daban-daban, wato iya kudinka iya shagalinka.

Umar ya za6i fannin jarida kuma ya tsallake duk wani Abu da suke bukata, Digiri da wasu suke samu a shekara 4 zuwa 5, shi kuma ya same shi a sati 6.

Bayan ya biya kudi aka bashi komai na kammale Karatu sai yayi fargaban ko takardun zasu iya zama na bogi.

Abun mamaki kuma sai ya gano makarantar tanada lasisin karantarwa na Gobnatin Najeriya da Kuma jamhuriyyar Benin.

Wannan mutumin da kuke gani, shine ya sace budurwa ya kulle ta a gida tsawon shekara bakwai 7 ta Haifa masa Yara 3 batar...
29/12/2023

Wannan mutumin da kuke gani, shine ya sace budurwa ya kulle ta a gida tsawon shekara bakwai 7 ta Haifa masa Yara 3 batare da aure ba.

Matashin Dan kimanin shekara talatin 30 Mai suna Joe Abdulmumin ya boye Budurwan mai suna Rabi'ah Salisu Yar kimanin 22 a gidansu Dake unguwar dogarawa a karamar hukumar sabon gari har tsawon shekara 7 da s**a wuce.

Inda Budurwan Rabi'ah ta haifa masa Yara 3, biyu mata daya 1 Kuma namiji.

A hiran da hukumar Hisbah tayi da mahaifin matashin wanda shi makaho ne, yace yayi iya kokarin sa don yaron ya maida yarinyar gidan su amma yaki har ya hakora ya dena magana.

Mahaifin ya kara dace cewa shi asalinsa dan garin madobi ne dake Jihar kano amma shi ba musulmi bane kirista ne.

Cikin binciken da Hisbah ta gudanar ta gano ƴaƴan Rabi'ah, Malam Abdullahi Salisu, inda a jawabinsa yace shekaru bakwai kenan suna neman ƙanwarta su da ta baro gida daga gidan su a unguwar jaba daga nan basu ƙara jin ɗuriyar ta ba sunyi adduah daga baya s**a mayar da komai zuwa ga mahaliccin su.

Wannan magidanci da kuke gani shine yasa akayi wa kansa keji don ya dena shan sigari.Mutumin dan asalin kasar turkey ya ...
26/12/2023

Wannan magidanci da kuke gani shine yasa akayi wa kansa keji don ya dena shan sigari.

Mutumin dan asalin kasar turkey ya kirkiri yi wa kansa keji ne don ya bar shan taba.

Magidancin Mai suna Ibrahim Yucel ya shafe shekara ashirin da shida 26 yana Shan sigari.

A kalla a kullum ya kan shanye kwali biyu sabida yanda abun ya zama masa jiki.

Yayi yinkurin daina shan taba ne bayan da taba yayi ajalin mahaifinsa a shekarun baya da s**a wuce.

Dalilinsa na daura aniyar Dena sha kenan don gujewa irin illolin da take yi a garkuwan jikin Dan Adam.

Ya bijiro da wannan kejin kayin ne don hana sha, sannan yasa kwado ya kulle ya baiwa matarsa makullin.

Wanda takan bude shine kawai a lokacin da zai zaa ci abinci don gudun kada ya sha taba.

Wannan tsoho da kuke gani shine yayi shekara 50 hamsin be saukar da hannunsa ba.Amar Bharati kenan na kasar indiya, Mist...
25/12/2023

Wannan tsoho da kuke gani shine yayi shekara 50 hamsin be saukar da hannunsa ba.

Amar Bharati kenan na kasar indiya, Mista Bharati yayi fice wajen akidarsa na Hindu.

Sannan dalilinsa na daga hannunsa na dama har tsawon shekara 50 hamsin shine don neman yanci da zaman lafiya a duniya baki daya.

Yayi fice wajen gugurmaya har ya shiga cikin kambun tarihi na daga hannu har tsawon shekara hamsin 50.

Wannan mutumin da kuke gani matarsa ce ta masa wanka da tafasasshen ruwan zafi bayan ya kwanta bacci.Dalilinta nayi wann...
25/12/2023

Wannan mutumin da kuke gani matarsa ce ta masa wanka da tafasasshen ruwan zafi bayan ya kwanta bacci.

Dalilinta nayi wannan danyen aikin shine wai don ya hana ta binsa zuwa wajen bikin daurin aure.

24/12/2023
Sabo da bushewa da kyekashewar zukatan su kan aikata alfasha sun kalle ka a ɗakin Allah sai s**a ji wa ran su ba Ƙa'aba ...
23/12/2023

Sabo da bushewa da kyekashewar zukatan su kan aikata alfasha sun kalle ka a ɗakin Allah sai s**a ji wa ran su ba Ƙa'aba ba ce hotel ce...!!!
-----------

Sun ajiye dukkan matakai na shari'a da jawaban zahiri a kan abinda s**aji daga masu bincike da hukumomi da kuma bayanan da s**a fito daga wadanda s**a aikata laifi sai s**a ajiye wannan s**a gaskata abinda munanan zuciyoyin su s**a sawarta musu.

Maimakon su bar mu da zafin ciwon da yake mana radadi sai s**a rubanya mana zafi kan zafi.

Mun samu addu'oi da jaje daga mutanen kirki, amma togaciyar Allah bata isa fasikai da annamimai ba.

Ko kadan mutumin kirkiri bai taba kasancewa a wannan sahu ba, godiya ga Allah da tushen zancen su ya zama daga mafi sharri da fasikanci a wannan saha shine sila kuma tushen zancen.

Da na kalli fiskokin masu dagewa da yada shi sai naga mutane biyu ne rak daga fasiki sai jahili.

Allah ka yi yafiya ga wanda rashin sani ya kwasa tare da togaciyar ka a kan sa, ka yi sakayya tsakanin mu da masu ganganci da bushewar ido.

Muna kara jan hankalin mutane, kada ku mance duk abinda kuka fadi na karya game da wannan bawan Allah walhi sai kun bayy...
23/12/2023

Muna kara jan hankalin mutane, kada ku mance duk abinda kuka fadi na karya game da wannan bawan Allah walhi sai kun bayyana shi a ranar kiyama".

Allah ya jikansa da rahama

Ana ku binciken wa ya gaya maku cewa shi NAFIU ya gayawa wa Hafsat Zaiyi aure??Still a cikin naku tsararren labarin, kun...
23/12/2023

Ana ku binciken wa ya gaya maku cewa shi NAFIU ya gayawa wa Hafsat Zaiyi aure??

Still a cikin naku tsararren labarin, kun mance da cewa shi mijin Hafsat shine ya kira gidansu NAFIU yayi karya cewa Nafiu ya rasu bayan surgery da aka masa!!

Shi kuma mijin Hafsat shine yasa aka yi masa lifafa bayan Hafsat ta kashe Nafiu, shine still yaki yarda a bude gawarsa a duba.

Shin wani irin lusarin miji ne wannan?

Wannan mata da kuke gani itace muguwar matar da ta kashe abokinmu Nafiu Hafiz Gorondo.Sun hada kai ne da maigidan ta s**...
22/12/2023

Wannan mata da kuke gani itace muguwar matar da ta kashe abokinmu Nafiu Hafiz Gorondo.

Sun hada kai ne da maigidan ta s**a kashe shi Kuma s**ayi kokarin rufe abun.

Matar ta amsa da bakinta cewa ita ta caccakka masa wuka a wuya da kahon zuciyar sa da kuma gefen cikinsa har ya mutu.

Yanzu haka mutum uku suna hannun jamian tsaro mijin da matar da Kuma wanda ya tattare shi ya sa masa lifafa da sunan ya masa wanka.

Baza mu dinga zuba Ido ana irin wannan kisan Gillan kuma ana barin masu aikatawa su sha ba.

Yanzu da ace mahaifin Nafiu be duba gawar dansa da kyau ba da baza su gane cewa kashe shi s**ayi ba.

Autopsy da akeyi na binciken sanadiyyar mutuwar mutum ma yana da mahimmanci.

Mu musulmai sabida an San mu da tawakkali ana amfani dashi ana cin zarafin mu.

Bamu yarda da Wannan kisan Gillan da akayi wa Nafiu ba ko ma menene be cancanci a masa irin wannan kisa ba.

Muna neman Gwabnati da ta kwato masa hakkinsa agun wannnan azzaluman mutanen.

Allah ya jikansa Kuma yasa ya huta, Allah ya gafarta masa zunubansa.

Muna kira ga Gobnatin Jihar Kano da ta kwatanta adalci ga wannan bawan Allah, dan uwanmu Nafiu Hafeez Gorondo wanda aka ...
21/12/2023

Muna kira ga Gobnatin Jihar Kano da ta kwatanta adalci ga wannan bawan Allah, dan uwanmu Nafiu Hafeez Gorondo wanda aka zalinta akayi masa kisan gilla.

Muna fatar Allah ya jikansa da rahama ya gafarta masa zunubansa, ya saka masa da gidan Aljanna.

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mujahid Saleh Saad - Dan maliki posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mujahid Saleh Saad - Dan maliki:

Share