Sir bangiss

Sir bangiss Assalamu yan uwana maza da Mata inamuku fatan alheri ni babangida daga jahar gombe state

SHAKAKIN MAZA DAN SHEHU KUNUN GABARUWA CIKA CIKI KAS MAKOGWARO:πŸ˜πŸ‘‘πŸ”₯Allah Ya Kara Shiga Tsakanin Nagari Da Mugu, Allah Ya ...
21/10/2023

SHAKAKIN MAZA DAN SHEHU KUNUN GABARUWA CIKA CIKI KAS MAKOGWARO:πŸ˜πŸ‘‘πŸ”₯

Allah Ya Kara Shiga Tsakanin Nagari Da Mugu, Allah Ya Kara Shiga Cikin Dukkan Lamuran Sarki, Allah Ya Karawa Sarki Kwazo Da Himma Cikin Aikin Mulkinsa..πŸ™πŸ‘βœŠπŸ€²πŸ”₯πŸ‘‘πŸ˜

21/10/2023

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM πŸ™πŸ™

NASIHA CE...

"Mafi Yawancin Asalin Fitina da Rashin Jituwa Ko rashin fahimtar Juna tsakanin Al'ummah Ya kan samo asaline Daga Zargi da kuma Hassada.

1. Shi Zargi Guba ne dake Gurbata Zamantakewa da 'Yan uwantaka da Abotaka da Makwabtaka Wanda aka ginata shekara da shekaru.

2. Ita Kuma Hassada wuta Ce dake cinye soyayya da Kuma Kaunar Juna, Ta rushe Kyawawan Ayyuku Na Alheri Ga Mai yinta Ta Kuma jinkirta masa Tunani.

Ya Ubangijin Annabi Muhammadu (S.A.W) Ka Kiyayemu Damu da Zuri'armu Don Darajar Annabi Muhammadu (S.A.W).

Ina Muku Fatan Alheri Da Kuma Barka Da Safiya.πŸ™πŸ™πŸ™

19/10/2023

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM πŸ™πŸ™πŸ™

NASIHA CE:

HATSARIN ZALUNCI:

Abu Umamah Al-BΓ‘hiliy _radhiyallahu anhu_ ya ruwaito daga Annabi sallallahu alaihi wasallam cewa: "Duk wanda ya kwaci hakken wani mutum musulmi ta hanyar rantsuwa (a kotu) to, tabbas Allah ya wajabta masa shiga wuta kuma ya haramta masa shiga aljanna". Sai wani mutum ya ce: Ko da abin dan kadan ne? Sai Manzon Allah ya ce: "ko da karan aswaki ne". Sahihu Muslim: 137

Sharhi:
Hadisin ya kumshi tsoratarwa daga zalunci komai kankantar sa.
Idan zalunci ya hadu da raina Allah; ta kai mutum zai sa sunan Allah a gaban zaluncinsa saboda rashin jin tsoron Allah da karancin girmama shi, to wannan ya gama shiga mahalaka.

Allah ya kiyaye mu.

Ina Muku Fatan Alheri Da Kuma Barka Da Safiya.πŸ™πŸ™πŸ™

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM RANAR DA QASA ZATA TSAGE!! Farkon wanda Qasa zata tsage masa ya fito ta cikinta shine Annabi...
18/10/2023

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

RANAR DA QASA ZATA TSAGE!!

Farkon wanda Qasa zata tsage masa ya fito ta cikinta shine Annabi Muhammadu (S.A.W) Shugaban halittun farko da Qarshe.

Yana fitowa zai tarar da Mala'ika Jibreelu da Mika'ilu suna tsaye akan Qabarinsa mai daraja (S.A.W) Yana haske yana Qamshi.

Farkon abinda zai tambayesu shine "YA JIBREELU INA AL'UMMATA?".

Nan zasu nuna masa wajen Abubakar da Umar da sauran Manyan Sahabbansa ya tashesu. Daga nan kuma sai sauran mutane.

Idan mutane suna fito daga cikin Qaburburansu zasu ga wata irin duniya ce wacce basu saba ganinta ba. Domin awannan lokacin zasu ga duniyar ta zama fili ne tas wa da babu tudu ko gangara acikinsa.

Dukkan duwatsun duniyar an riga an nikesu. Duk wani tudu an riga an bajeshi. Dukkan bishiyoyi sun Qone sun rube babu alamarsu. Dukkan gine-gine kuma sun rushe babu koda alamar wani birni ko kauye. Kuma dukkan Koguna da rafuka dun Qafe, suna cin Wuta!!!

Sama zata kekkece, Taurari zasu dusashe su gurbace. Rana da farin wata zasu zamanto Bakake wuluk!!! Babu haske tare dasu.

Awannan lokacin ne ana cikin wannan tashin hankalin Mala'iku zasu kora dukkan mutane zuwa ga filin hisabi. Kowa yana dauke da Lodin zunuban da ya aikata..

Wadansu zasu hau Buraqah Su tafi zuwa inuwar al'arshi. anan zasu zauna suna hutawa har a Qare hisabi ga Mutane. su ba za'ayi. usu hisabi ba.

Wadansu kuma awannan ranar za'a tashesu acikin mummunar Siffa. Masu cin kudin ruwa da masu cin dukiyar marayu duk zasu kasance da manyan tumbi, wuta tana cinsu ta cikin cikinsu. Suna eehu amma babu mai taimakonsu.

Masu Gulma da yarfe da Qazafi, za'a tashesu bisa Siffar karnuka. Kuma laifukansu zasu zama tamkar manyan duwatsun duniya agabansu.

YA ALLAH KASA MU CIKA DA IMANI BIJAHI RASULILLAHI (S.A.W).

18/10/2023

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

MU'UJIZAR DAKE CIKIN ADDU'ARSA (S.A.W)

Wani Sahabi mai suna Thabit bn Yazeed (radhiyal-Lahu anhu) yazo wajen Manzon Allah (S.A.W) yace "Ya Rasulallahi Qafata guda daya gurguwa ce, bata ta'ba kasa.

Nan take Manzon Allah (S.A.W) yayi masa addu'a, kuma ya warke, ta dawo daidai da 'dayar.

Imamul Tabaraniy ne ya ruwaitoshi acikin Musnadush Shamiyyin da Albarudiy acikin Alma'arifah.

Salati da amincin Allah su tabbata bisa Mafificin Annabawa da Manzanni (S.A.W) Shugabanmu Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa tsarkaka da sahabbansa gwargwadon matsayinsa da darajojinsa awajensa.

GARBA SADAUKI GARBA GAGARE GARBA RUWAN DARE DAMA DUNIYA:🦁πŸ”₯πŸ‘‘Allah Ya Kara Tsole Idanun Maqiyan Sarki, Allah Duk Wanda Ya ...
05/10/2023

GARBA SADAUKI GARBA GAGARE GARBA RUWAN DARE DAMA DUNIYA:🦁πŸ”₯πŸ‘‘

Allah Ya Kara Tsole Idanun Maqiyan Sarki, Allah Duk Wanda Ya Damu Sarki Allah Ya Dameshi, Allah Ya Karawa Sarki Lafiya Da Kwanciyan Hankali.πŸ™πŸ‘βœŠπŸ€²πŸ”₯πŸ‘‘πŸ¦

RUWA DA KADA DA DAURINA MAI WANKA KA KIYAYE:🐘πŸ”₯πŸ‘‘πŸ™πŸ€²Allah Ya Kara Daura Sarki Akan Maqiyansa,  Allah Yasa Sarki Ya Gama Da ...
04/10/2023

RUWA DA KADA DA DAURINA MAI WANKA KA KIYAYE:🐘πŸ”₯πŸ‘‘πŸ™πŸ€²

Allah Ya Kara Daura Sarki Akan Maqiyansa, Allah Yasa Sarki Ya Gama Da Duniya Lafiya Cikin Nasarori Masu Tarun Yawa, Ya Kara Tsare Gaban Sarki Da Bayansa.πŸ˜πŸ€²πŸ™πŸ‘‘πŸ”₯

26/09/2023

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

KUNJI MANZON ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM

Bayan an kammala yaqin Hunainu, yayin da Manzon Allah (S.A.W) yazo rabon kayan ganimah, sai ya rarrabata atsakanin mutanen Makkah da sauran Qabilun larabawa wadanda basu dade da shiga musulunci ba.

Mutanen Madeenah kuwa (AL ANSAR) bai basu komai ba. don haka sai wasu daga cikinsu suke mamakin mai yasa Manzon Allah (S.A.W) bai raba ganima dasu ba? Alhali tare dasu akayi gwagwarmayar nan!!

Da maganar tazo kunnensa (S.A.W) sai ya tarasu gaba dayansu waje guda yayi musu jawabi mai ratsa zukata, sannan daga karshe yace musu :

"SHIN YANZU BA ZAKUYI FARIN CIKI BA, SAURAN MUTANE ZASU KOMA GUDAJENSU DA AWAKI DA TUMAKAI DA ZINARE DA AZURFA, KU KUMA ZAKU KOMA GIDANKU TARE DA MANZON ALLAH!!!".

Sai s**a fashe da kuka suna cewa "Munyi farin ciki mun yarda da Manzon Allah (S.A.W) Shine rabonmu, shine kasonmu!!".

Allah yi salati da amincinka mafi girma bisa Annabinka mafi daraja, Shugaban mutanen farko dana karshe, mai tutar godiya aranar tsaiwa, Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa masu daraja da Sahabbansa madaukaka da dukkan mabiya bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Amin Ya Hayyu Ya Qayyum πŸ™

24/09/2023

οΌ­οΌ΅οΌ¨οΌ‘οΌ­οΌ­οΌ‘οΌ€οΌ΅οΌ²
οΌ²οΌ‘οΌ³οΌ΅οΌ¬οΌ©οΌ¬οΌ¬οΌ‘οΌ¨
πŸ₯°βœŠ

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM NASIHA CE:Ganin Girman ZunubiAl-Hasan Al-Basriy _rahimahullah_ ya ce: Mutum yakan yi wani zu...
24/09/2023

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

NASIHA CE:

Ganin Girman Zunubi

Al-Hasan Al-Basriy _rahimahullah_ ya ce: Mutum yakan yi wani zunubi da zai kasa mantawa, yana ta jin tsoron wannan zunubin yana damuwa a zuciyarsa har sai wannan zunubin ya shigar da shi aljanna (Saboda girman da-na-sanin sa). KitΓ buz Zuhd na Imam Ahmad 1604.

Ibnul Qayyim _rahimahullah_ ya ce: "Idan Allah yana son alheri ga mutum sai ya cire masa ganin alhairansa daga zuciyarsa b***e kuma ya furta su da harshensa. A maimakon haka sai ya yi ta nuna masa zunubansa ya rika kallon su (yana da-na-sani har su shigar da aljanna) Dariq Al-Hijrtain, na Ibn A-Qayyim, shafi na 310.

Allah Yasa Mudace Duniya Da Lahira Bijahi Rasulillahi (S.A.W).

A KIYAYI SARKI A KIYAYI DODO:πŸ˜πŸ‘‘πŸ”₯Allah Ya Kara Dafawa Sarki Cikin Dukkan Lamuransa, Allah Yasa Lahiran Sarki Tafinan, All...
23/09/2023

A KIYAYI SARKI A KIYAYI DODO:πŸ˜πŸ‘‘πŸ”₯

Allah Ya Kara Dafawa Sarki Cikin Dukkan Lamuransa, Allah Yasa Lahiran Sarki Tafinan, Allah Yasa Sarki Ya Gama Da Duniya Lafiya.πŸ€²βœŠπŸ‘πŸ™πŸ‘‘πŸ”₯🐘

Address

Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sir bangiss posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share