27/02/2026
DA DUMI-DUMI: Gidauniyar Farfesa Pantami Ta Ƙaddamar Da Raba Kayayyakin Abinci Fiye Da Buhu 12,500 Da Kuma Kuɗi Naira Miliyan 33,750,000 Ga Malaman Addini A Gombe
Gidauniyar Professor Isa Ali Pantami (PIP Foundation) ta ƙaddamar da raba kayan abinci kusan buhu 12,500 da s**a haɗa da shinkafa, masara, gero, s**ari, taliya (spaghetti da macaroni), da sauran su a dukkan ƙananan hukumomi 11 na jihar Gombe.
Aikin raba kayayyakin abincin yana gudana ne ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abubakar Ahmad Walama (Sarkin Malaman Gombe), Dr. Abubakar Saidu (Tsohon babban daraktan asibitin koyarwa na tarayya dake Gombe), Arch. Dahiru Saidu, da kuma uwar gidan Farfesa Isa Pantami, tare da haɗin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki, matasa, da mata.
Kayan abincin da ake rabawa sun haɗa da buhu 3,500 na shinkafa mai nauyin 50kg, buhu 1,000 mai nauyin 25kg, da kuma fiye da buhu 2,000 mai nauyin 10kg. Bugu da ƙari, akwai fiye da buhu 1,000 na gero da buhu 1,000 na masara. Sauran kayan sun haɗa da buhu 900 na kus-kus, fiye da buhu 2,500 na semovita, katan 500 na macaroni, da kuma fiye da buhu 150 na s**ari.
Ana raba waɗannan kayayyaki ne ga shugabannin addini, shugabannin al’umma, ‘yan siyasa, matasa, mata, marayu, da kuma mutane masu buƙata ta musamman. Kwamitin raba kayan ya tabbatarwa da jama’a cewa za a raba abincin ne a dukkan ƙananan hukumomi 11 na jihar, sai dai saboda yawan jama’a, ba kowa ne zai iya samu ba, sai waɗanda Allah ya ƙaddara suna cikin jerin waɗanda za su amfana.
Farfesa Isa Ali Ibrahim (Pantami) ya shafe shekaru da dama yana tallafawa jama’a a lokacin watan Ramadan, inda adadin tallafin yake sauyawa shekara bayan shekara. Waɗanda s**a amfana sun nuna godiyarsu ga wannan karamci wanda ya kawo farin ciki ga iyalansu, sannan sun yi wa Farfesa da tawagarsa addu’ar Allah ya saka musu da mafificin alkhairi.
Gidauniyar Farfesa Isa Pantami (PIP Foundation) ta ware zunzurutun kuɗi har Naira miliyan 33,750,000 domin tallafawa malaman addini a Gombe. Gidauniyar ta daɗe tana tallafawa malaman addini a Gombe da ma Najeriya baki ɗaya. A shekarar da ta gabata, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ta hanyar wannan gidauniya, ya tallafa wa malaman Gombe da Naira miliyan 27 a jihar Gombe kaɗai, baya ga sauran tallafi. Dr. Umar Garba Dokaji ne yake jagorantar aikin raba tallafin ga malaman addinin.