Muryar Nigeria

Muryar Nigeria Shafi ne dake kawo maku abubuwan karuwa na yau da kullun. Domin kawo maku ingantattun labarun Arewacin Najeriya da Najeriya baki ɗaya.

DA DUMI-DUMI: An sako El-Rufai, ya dawo gida domin halartar jana’izar mahaifiyarsa.
27/03/2026

DA DUMI-DUMI: An sako El-Rufai, ya dawo gida domin halartar jana’izar mahaifiyarsa.

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN: Ku sanya Alaramma Ahmad Sulaiman cikin addu'o'inku. Biyo bayan mummunan hatsarin mo...
19/03/2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN: Ku sanya Alaramma Ahmad Sulaiman cikin addu'o'inku. Biyo bayan mummunan hatsarin mota da ya gamu da shi a jiya, yanzu haka yana asibiti inda aka shigar da shi na'ura ana duba lafiyar sassan jikinsa sak**akon buguwa da ya samu.

Allah ya ba shi lafiya.

Shugaba Tinubu ya zaɓi Gwamna Dauda Lawal cikin masu yi masa rakiya zuwa BirtaniyaGwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, na...
16/03/2026

Shugaba Tinubu ya zaɓi Gwamna Dauda Lawal cikin masu yi masa rakiya zuwa Birtaniya

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, na cikin tawagar da za ta raka Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, domin wata ziyara ta gwamnati zuwa Birtaniya.

Shugaban ƙasar tare da mai dakinsa da sauran mambobin tawagar gwamnati za su tashi daga Abuja ranar Talata domin fara ziyarar, inda King Charles III zai karɓi bakuncinsu a Windsor Castle daga ranar 18 zuwa 19 ga Maris, 2026.

A wata sanarwa da kakakin gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an ce ziyarar na da nufin ƙarfafa dangantakar diflomasiyya tsakanin Nijeriya da Birtaniya, tare da duba damar haɗin gwiwa a fannoni k**ar shige da fice, kasuwanci, zuba jari da mu’amalar al’adu.

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan ziyara za ta ba Gwamna Dauda Lawal dama ta kulla sabbin alaƙa da jawo masubzuba jari, wanda zai iya samar da fa’idar tattalin arziki ga Jihar Zamfara.

DA DUMU DUMINSANASARA DAGA ALLAHJiya da misalin karfe 7:50 na yamma, jami’an ‘yan sanda sun k**a wani yaro matashi dan s...
11/03/2026

DA DUMU DUMINSA

NASARA DAGA ALLAH

Jiya da misalin karfe 7:50 na yamma, jami’an ‘yan sanda sun k**a wani yaro matashi dan shekara 25 mai suna Mannir Adam mai shekaru 25, mazaunin kauyen Yankuzo, Karamar Hukumar Tsafe Jihar Zamfara, wanda yake tuka babur kirar Boxer mai launin ja

An k**ashi ne a kan babbar hanyar Gusau–Funtua, a shingen bincike na 'Yankara yana dauke da alburusai guda dari takwas (800) na bindigar AK-47 wadanda ya boyesu a cikin tankin man fetur na babur dinsa

Binciken farko ya nuna cewa matashin yana dauko mak**an ne tun daga Unguwar Bawa a Karamar Hukumar Saminaka ta Jihar Kaduna, kuma yana kan hanyarsa ta zuwa kauyen Kucheri a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara domin ya mikasu zuwa ga barayin daji

Jama'a kun ga dai yadda wasu gurbatattu da muke rayuwa tare da su a cikin gari suke taimakon barayin daji wajen isar musu da mak**an da zasu dinga kashe al'umma da shi

Lokaci yayi da Gwamnatoci zasu yi doka na Kotun tafi da gidanka, duk wanda jami'an tsaro s**a k**a ya dauko kayan ta'addanci zai kai wa barayin daji, to ayi amfani da kayan da ya dauko a sashi yayi baccin da babu farkawa anan duniya

Idan akayi haka za'a jefa babban tsoro a cikin zukatan mutane masu tunani shiga wannan bakar sana'a

Muna fatan Allah Ya cigaba da tona asirin masu taimakon 'yan ta'adda ta kowace irin hanya.

Da Dumi-DumiGwamnan jihar Zamfara Dauda ya bar PDP ya koma APC
09/03/2026

Da Dumi-Dumi

Gwamnan jihar Zamfara Dauda ya bar PDP ya koma APC

LABARI MAI DADIYanzun nan Kotu ta yanke hukunci a kan shari'ar da hukumar NDLEA take yi da Sarkin Yakin Nigeria DCP Abba...
05/03/2026

LABARI MAI DADI

Yanzun nan Kotu ta yanke hukunci a kan shari'ar da hukumar NDLEA take yi da Sarkin Yakin Nigeria DCP Abba kyari

Shari'a na farko a kan Money Laundry wato tuhumar da NDLEA suke yiwa Abba Kyari na mallakar kudin haram, wanda ya sa s**a rufe gidajensa da duk wani kadarori da ya mallaka shi da kannensa

To yanzun nan Alkali ya wanke DCP Abba Kyari daga dukkan zargi na mallakar kudin haram, ya kori karan NDLEA gaba daya

Wannan babban nasara ce ga Sarkin Yakin Nigeria DCP Abba Kyari
Masu aikata ta'addanci a Nigeria kun shiga uku dodon ku na dab da fitowa

Alhamdulillah🙏

ABIN MAMAKIYanzu nake ganin sanarwa wai kungiyar Izala bangaren Jos ta dakatar da Sheikh Alkali Zaria daga yin Tafsirin ...
03/03/2026

ABIN MAMAKI

Yanzu nake ganin sanarwa wai kungiyar Izala bangaren Jos ta dakatar da Sheikh Alkali Zaria daga yin Tafsirin Ramadan da yake gabatarwa a jihar Yobe

Wai wannan dakatarwan da aka masa tana da nasaba da caccakar Shugabannin Demokradiyya da yayi a kwanakin nan

Sannan ance wai Shugaban Majalisar Malaman Izalar Jos Sheikh Sani Yahaya Jingir ya kira Malamin zuwa Jos domin yaja kunnensa akan zafafawa da yake, shiyasa kwana biyu aka ga baya yin Tafsiri

Idan wannan labari da aka bayyana ya tabbata gaskiya to ba shakka ba'a kyauta ba, su 'yan siyasar Demokradiyya babu addini a tsarinsu, don Malami ya caccakesu bai zama dalilin da zai sa a hanashi wa'azi ba

Allah Ya sauwake

Tinubu ya dakatar da sallamar manyan jami’an ƴansanda 30 bayan naɗin sabon mukaddashin IG Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinu...
27/02/2026

Tinubu ya dakatar da sallamar manyan jami’an ƴansanda 30 bayan naɗin sabon mukaddashin IG

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya dakatar da shirin tilasta wa manyan jami’an rundunar ’yansanda kusan 30 yin ritaya, bayan sauyin shugabanci da aka samu a hedikwatar rundunar k**ar yadda jaridar Sahara Reporters ta rawaito.

Matakin ya biyo bayan miƙa ragamar aiki da tsohon Sufeto Janar na ’yansanda, Kayode Egbetokun, ya yi ga wanda ya gaje shi a matsayin mukaddashin Sufeto Janar, Tunji Disu.

Naɗin sabon mukaddashin IGP ya sake tayar da muhawara a faɗin ƙasa kan al’adar da ake bi a rundunar, inda sauyin shugabanci kan haifar da tilasta wa manyan jami’ai, musamman Mataimakan Sufeto Janar (DIGs) da Mataimakan Sufeto Janar na Musamman (AIGs), yin ritaya domin daidaita tsarin jagoranci.

Rahotanni sun nuna cewa an tsara wani shiri da zai kai ga sallamar kimanin DIGs da AIGs 30 bayan sauke Egbetokun daga muƙaminsa. Sai dai an ce Shugaba Tinubu ya shiga tsakani domin dakatar da aiwatar da shirin, lamarin da ya kawo sauyi a cikin tsarin da aka saba.

Wata majiya ta ce matakin shugaban ƙasar ya kawo kwanciyar hankali a tsakanin manyan jami’an rundunar, musamman ma waɗanda ake zargin za su fuskanci ritaya ta dole.

A cikin jerin sunayen da ake yaɗawa a rundunar, an ambaci cewa akalla DIGs takwas ne ake sa ran za a yi wa ritaya domin daidaita sabon tsarin jagoranci. Daga cikinsu akwai Yahaya Abubakar, Adebola Hamzat, Adebowale Williams, da Frank Mba.

Har zuwa lokacin fitar da wannan rahoto, rundunar ’yansanda ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan dakatar da shirin ba.

DA DUMI-DUMI: Tsohon sufeto janar na 'yan sanda Kayode Egbetokun, ya bukaci magajinsa da ya dora daga inda ya tsaya.  Me...
25/02/2026

DA DUMI-DUMI: Tsohon sufeto janar na 'yan sanda Kayode Egbetokun, ya bukaci magajinsa da ya dora daga inda ya tsaya.

Me za ku ce?

"Ina goyon bayanka, ka yi kokari wajen magance matsalar tsaro da Nijeriya ke fuskantar" - Tinubu Shugaban Kasa, Bola Ahm...
25/02/2026

"Ina goyon bayanka, ka yi kokari wajen magance matsalar tsaro da Nijeriya ke fuskantar" - Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya umurci Mukaddashin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Olatunji Disu, da ya dauki matakan gaggawa domin farfado da zaman lafiya da karfafa tsaro a fadin Najeriya.

RAN MAZA YA BACI: Mai Taimakawa Gwamnan Bauchi Kan Harkokin Matasa, Bala Rambo Kenan Cikin Shirin Shiga Daji, Domin Tunk...
24/02/2026

RAN MAZA YA BACI: Mai Taimakawa Gwamnan Bauchi Kan Harkokin Matasa, Bala Rambo Kenan Cikin Shirin Shiga Daji, Domin Tunkarar 'Ÿan Bìn̈digà, Inda Ya Ce Duk Wanda Ya Shirya Ya Biyo Shi Su Tafi

Wace fata za ku yi masa?

Yanzu-Yanzu: Shugaba Tinibu Ya Nada AIG Olatunji Rilwan, a matsayin sabon sufeton ƴan Sandan Najeriya.
24/02/2026

Yanzu-Yanzu: Shugaba Tinibu Ya Nada AIG Olatunji Rilwan, a matsayin sabon sufeton ƴan Sandan Najeriya.

Address

Gwarinpa
420241

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share