18/05/2026
Hukumomin ƙasar Saudiyya sun sanar da ganin jinjirin watan Dhul Hijjah a yau Lahadi.
Cikin wata sanarwa da shafin Haramain ya wallafa a shafinsa na X, ya ce gobe Litinin ne ɗaya ga watan na babbar salla.
Hukumomin na Saudiyya sun kuma ce ranar Talata 26 ga watan Mayu ne za a yi tsayuwar Arafa, yayin da za a yi Idin babbar sallah ranar Laraba 27 ga watan na Mayu.