KGT News

KGT News KGT News na kawo muku sahihan labarai da s**a shafi tsaro da lafiya a Najeriya da duniya baki daya.

Rundunar sojin samma ta kashe 'yan ta'adda da dama, a NejaRundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta ce ta kashe 'yan ta'a...
25/05/2026

Rundunar sojin samma ta kashe 'yan ta'adda da dama, a Neja

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta ce ta kashe 'yan ta'adda da dama kuma ta hana kai hari da aka shirya a Jihar Neja yayin wasu jerin hare-hare.

Dubban mutane sun yi tattaki a Madrid suna neman Firayim Ministan Spain ya yi murabus kan zarge-zargen cin hanci da rash...
23/05/2026

Dubban mutane sun yi tattaki a Madrid suna neman Firayim Ministan Spain ya yi murabus kan zarge-zargen cin hanci da rashawa.

Rundunar 'yan sandan jihar Enugu ta ce jami'anta sun kai samame a wata maboya da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a ...
21/05/2026

Rundunar 'yan sandan jihar Enugu ta ce jami'anta sun kai samame a wata maboya da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a wani daji da ke kan iyakar Amufie-Obollo-Afor a karamar hukumar Igbo-Eze, inda s**a kwato harsasai, babur da sauran kayayyaki bayan musayar wuta da wadanda ake zargin.

‎A cikin wata sanarwa da Daniel Ndukwe, mai magana da yawun rundunar ya fitar a ranar Laraba, ya ce an gudanar da aikin ne a ranar Lahadi da misalin karfe 7:40 na yamma bisa umarnin Mamman Giwa, kwamishinan 'yan sandan jihar.

Siminalayi Fubara, gwamnan jihar Rivers, ya janye daga zaben fidda gwani na gwamna na jam'iyyar APC a jihar.‎‎Fubara ya ...
20/05/2026

Siminalayi Fubara, gwamnan jihar Rivers, ya janye daga zaben fidda gwani na gwamna na jam'iyyar APC a jihar.

‎Fubara ya ba da sanarwar janyewarsa daga gasar a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, yana mai jaddada cewa ya janye ne saboda gamsuwa da sadaukarwa don jiharsa ta ci gaba da zaman lafiya da hadin kai.

Femi Otedola, shugaban First HoldCo, ya bayyana cewa zai zuba jarin dala miliyan $100 a cikin matatar Dangote.‎‎Otedola ...
20/05/2026

Femi Otedola, shugaban First HoldCo, ya bayyana cewa zai zuba jarin dala miliyan $100 a cikin matatar Dangote.

‎Otedola ya sanar da shirye-shiryensa a ranar Laraba bayan ya jagoranci manyan jami'an First HoldCo zuwa matatar Dangote.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai Barau Jibrin, Yahaya Bello, tsohon gwamnan Kogi, da Nasir Daura, kakakin majalisa...
18/05/2026

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai Barau Jibrin, Yahaya Bello, tsohon gwamnan Kogi, da Nasir Daura, kakakin majalisar dokokin jihar Katsina, sun samu nasarar lashe zabukan fidda gwani na sanata na APC a jihohinsu.

‎Barau ya lashe zaben fidda gwani na APC don yankin Sanatan Kano ta arewa gabanin babban zaben 2027, bayan wani taron tabbatarwa da aka gudanar a karamar hukumar Bichi.

Dan Buhari, Yusuf, ya lashe zaben fidda gwani na wakilai na APC da kuri’u 5,849Yusuf Buhari, ɗan tsohon shugaban Najeriy...
16/05/2026

Dan Buhari, Yusuf, ya lashe zaben fidda gwani na wakilai na APC da kuri’u 5,849

Yusuf Buhari, ɗan tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari, ya samu nasara a zaɓen fidda gwani na jam'iyyar APC na kujerar majalisar tarayya ta Sandamu/Daura/Mai'adua.

Yusuf Buhari ya samu kuri'u 5,849 inda ya kayar da Auwal Daura, wanda ya samu kuri'u 21.

Wata kotun a Kwara da ke Ilorin ta yanke hukuncin daurin rai da rai ga Ajiboye Olayinka, babban mai kula da Mission Hous...
14/05/2026

Wata kotun a Kwara da ke Ilorin ta yanke hukuncin daurin rai da rai ga Ajiboye Olayinka, babban mai kula da Mission House of Divine Land of Joy and Prayer Ministry, saboda yin fyade wa yara mata uku a harabar coci.

‎A ranar Laraba, Hammed Gegele, alkalin kotun, ya yanke wa Olayinka hukunci kan laifuka da dama da s**a shafi yin lalata da yara ƙanana ba bisa ƙa'ida ba, zubar da ciki ba bisa ƙa'ida ba, da kuma mallakar mak**ai ba bisa ƙa'ida ba.

13/05/2026

"Yadda aka kashe Mahaifina akan ido na", Salim Sunusi.

Salim Sunusi daya ne daga cikin wadanda s**a rasa iyayensu a harin da 'yan bindiga s**a kai 'Yank**aye a karamar hukumar Tsanyawa ranar Litinin.

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya mayar da martani ga masu s**arsa bayan ziyarar da ya kai wa shugab...
13/05/2026

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya mayar da martani ga masu s**arsa bayan ziyarar da ya kai wa shugaban APC, Farfesa Nentawe Yilwatda.

‎Mista Wike ya shaida wa 'yan jarida bayan duba ayyukan da ake yi a Abuja ranar Laraba cewa baya yin siyasar gaba.

Jami'an hukumar EFCC sun k**a Mustapha Abdullahi, babban daraktan Hukumar Mak**ashi ta Najeriya, bisa zargin aikata laif...
13/05/2026

Jami'an hukumar EFCC sun k**a Mustapha Abdullahi, babban daraktan Hukumar Mak**ashi ta Najeriya, bisa zargin aikata laifukan zambar kudi da s**a haura Naira biliyan 500.

‎Rahotanni sun ce an k**a Abdullahi a Abuja ranar Laraba kuma a halin yanzu yana tsare a hannun hukumar yaki da cin hanci da rashawa don ci gaba da bincike.

Address

Tukuntawa
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KGT News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KGT News:

Share