31/03/2026
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf tare da tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, sun gana da Shugaban Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Rt. Hon. Tadujjin Abbas jim kaɗan bayan wani muhimmin sauyi da ya faru a fagen siyasar Jihar Kano.
Gwamnan ya isa zauren Majalisar tare da tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje (Khadimul Islam), da Sanata Barau I. Jibrin, tare da Babban Daraktan Cibiyar Kula da Nagartar Ayyuka ta Ƙasa (NPC), Hon. Dr. Babba Danagundi NIM.
Ganawar ta zo ne a daidai lokacin da wasu ‘yan Majalisar Tarayya guda takwas daga Jihar Kano s**a sauya sheƙa daga Jam’iyyar NNPP zuwa Jam’iyyar APC mai mulki a ƙasa.
Wannan sauyin sheƙa ya ja hankalin masu ruwa da tsaki a harkar siyasa, inda ake kallon ganawar a matsayin wani muhimmin mataki na sake fasalin siyasar Jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.
Ayuba Jarimi
SSA Media to the DG NPC
Talata, 31 ga Maris, 2026.
By