21/01/2026
Kotu ta aike da Sheikh Ibrahim makwarari Gidan Yari sakamakon Gaza Cika sharuddan Beli
Wata kotu a Kano ta aike da fitavven malamin addinin Muslunci a Kano Sheikh Ibrahim makwarari Gidan gyaran hali sakamakon Gaza cika sharuddan Beli da kotun ta gindaya masa.
Tun da farko dai gwamnatin Kano karkashin ma'aikatar kasa ce ta shigar da malamin kara kotun kan laifin damfara da harkallar filaye.
Kwamishinan kasa na jihar Kano ya bayyana cewar akwai korafi jirage da dama a kan malamin kan sayarwa tare da harkallar filaye da cikin cikin ciniki, ya kara da cewar akwai filin da malamin ya sayarwa mutane 4.
Yanzu haka dai akwai wata shari'ar da ake yiwa malamin a wata kotu ta daban duk dai akan wannan laifi na harkallar filaye.
Kotun dai ta bayar da Berlin malamin akan kuɗi Naira miliyan 20, saidai Gaza cika sharuddan Berlin ne yasa aka Tisa ketare malamin zuwa gidan gayaran hali.