17/03/2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyaɗa Ranakun Alhamis Da Juma'a A Matsayin Hutu Domin Bikin Babbar Sallah
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Alhamis, 19 ga Maris, da Juma’a, 20 ga Maris, 2026 a matsayin ranakun hutu na ƙasa domin bikin Eid-el-Fitr, wanda ke nuna ƙarshen azumin watan Ramadan.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan a madadin Gwamnatin Tarayya, ta cikin wata sanarwa da Babbar Sakatariyar ma’aikatar, Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Talata.
A cikin sanarwar, ministan ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin Ramadan lafiya, tare da kira gare su da su ci gaba da riƙo da kyawawan ɗabi’u da aka koya a watan mai alfarma, kamar ƙauna, haƙuri, sadaukarwa, zaman lafiya da kuma taimakon juna.
Hakazalika, ya buƙaci ‘yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’o’i domin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa baki ɗaya.
Gwamnatin ta kuma shawarci al’umma da su gudanar da bukukuwan cikin natsuwa da lumana, tare da miƙa hannu ga marasa galihu domin su ma su ji daɗin bikin.
Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta na ƙarfafa haɗin kan ƙasa da zaman lafiya tsakanin dukkanin al’ummomin Najeriya.
Yaya kuke shirin gudanar da bikin Eid-el-Fitr bana? Kuma wane irin mataki kuke ganin ya kamata mu ɗauka domin tallafa wa marasa ƙarfi acikinmu a wannan lokaci?