08/02/2026
BATUN KHALIFA SANI (RTA)
*
**
***
Alhamdulillah tun bayan faruwar wannan lamarin, manyan mu basu yi ƙasa a gwiwa ba wurin taimakawa Ɗan'uwan su wato Maulana Khalifa Sani, mu kuma ƙorafin da muke yi shine a zahiri bamu san irin ƙoƙarin da suke yi ba b***e hankalin mu ya kwanta, tun daga nan ne suke sanar damu duk wani shiri nasu mai muhimmanci, ga yadda abubuwan suke:
1. Bayan faruwar lamarin, sun yi ƙoƙarin shige da fice a duk inda s**a san suna da alfarma don ganin an bar khalifa ya shaƙi iskar yanci, amma sashin manya a hukuma da gwamnati, sai s**a nemi ayi haƙuri a bari a gama bincike, da yake manyan mu masu biyayya ne kafin a tunzura su, sai s**a bi a haka, suna cigaba da bibiya don kar a juya gaskiyar mai gaskiya.
2. Bayan sojoji sun fitar da sunayen mutane 40 wayanda suke da hannu a sha'anin yunƙurin juyin mulkin, sai manyan mu s**a ga to ai rainin wayau ne tunda sun tabbatar ba ya ciki, meye na zaluntar sa haka ta hanyar ɓata masa lokaci da sunan sa?
3. Nan take masu ruwa da tsaki musamman shi Sayyadi Ibrahim ɗan Khalifa wanda aka k**a su tare a farko, s**a shigar da ƙara kotu.
A jiya Juma’a 6 ga Fabrairu, 2026, aka shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya (Federal High Court), Abuja, ƙarƙashin jagorancin Alƙali P. O. Lifu (JP), bisa tauye haƙƙin Maulana Khalifa na:
1. Mutunci (Dignity of Human Person)
2. Yancin walwala (Personal Liberty)
3. Adalcin shari’a (Fair Hearing)
4. Yancin motsi (Freedom of Movement)
Kotun ta umarci wayanda ake ƙara (Respondents) su bayyana dalilin tauye masa wannan haƙƙi da kuma abinda zai hana sakin sa, cikin 72 hours za suyi haka.
Kotun ta ayyana ranar 12 ga Fabrairu, 2026 ranar dawowa (Return Date), Kotun ta kuma bayyana cewa Idan s**a gaza nuna hujja mai gamsarwa, akwai yiwuwar kotu zata saki Maulana khalifa nan take ko ta bada belin sa.
4. Ina da dukkan takardun da kotu da bayar, don haka muna da tabbacin Insha Allah Khalifa a gida zai yi azumi albarkar Annabi ﷺ.
Amin ya Allah