25/06/2025
Arewa Media Writers Na Kira Ga Gwamnatin Tarayya Da Jihohin Filato Da Benue Kan Kisan Matasan Arewa
Daga Arewa Media Writers
Ƙungiyar marubutan Arewa a kafafen sada zumunta, Arewa Media Writers, ƙarƙashin jagorancin Comr Haidar H. Hasheem, ta bayyana damuwa da alhini game da kisan gillar da aka yi wa matasan Arewa a jihohin Filato da Benue a cikin makon nan, tare da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su gaggauta ɗaukar mataki.
A cewar ƙungiyar, a jihar Benue, an kashe Barhama Suleiman da Jamilu Ahmad, matasa 'yan asalin jihar Kano, bayan da wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne s**a tare motarsu s**a hallaka su. An gudanar da jana'izarsu a babban masallacin ƙasa da ke Abuja, inda manyan jami'ai ciki har da Nuhu Ribadu da Gwamna Abba Kabir Yusuf s**a halarta.
Haka kuma, a jihar Filato, matafiya daga Zaria, yawancinsu ’yan asalin Basawa, sun rasa rayukansu yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa bikin aure. Akalla mutum 12 ne s**a mutu a harin da aka kai a karamar hukumar Mangu.
Ƙungiyar ta bayyana cewa kisan gillar ba sabon abu ba ne, domin an dade ana kai wa 'yan Arewa hari a waɗannan yankuna, amma ba a ganin hukunci ko mataki daga hukumomi. Wannan shiru da sakaci na gwamnati yana ƙara nuna gazawar tsarin tsaro da rashin adalci ga ’yan Arewa.
Shin rayukan ‘yan Arewa ba su da ƙima? Ko kuwa gwamnati na da hannu a ciki ?
Arewa Media Writers ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da jihohin da abin ya shafa da su:
1. Gaggauta bincike da gurfanar da masu hannu a gaban kuliya.
2. Bayyana matsayi a fili kan kisan gillar da ake wa ‘yan Arewa.
3. Hukumomin tsaro (’Yan Sanda, DSS) su gudanar da bincike tare da bayyana sakamakon.
4. Majalisar dokoki ta kaddamar da bincike kai tsaye kan yawaitar kashe-kashen ’yan Arewa.
Ƙungiyar ta ƙara da cewa, irin wannan rashin adalci na barazana ga zaman lafiya da hadin kan Najeriya, don haka dole ne a tabbatar da cewa jinin ɗan Arewa yana da daraja kamar na kowa.
Idan gwamnati ba za ta kare rayukan ‘yan Arewa ba, mu da harshenmu da alkalumanmu za mu ci gaba da tashi tsaye har sai an yi mana adalci.
Rubutawa, Muhammad Kwairi Waziri, National Director Media And Publicity II Arewa Media Writers.