24/09/2024
Lokaci Ya Yi Da Matasa Za Su Karbi Ragamar Shugabancin Nijeriya A Zaben 2027, Inji Hon. Abdulrazaq Dahiru Kaita, Shugaban Tafiyar Matasa Na Katsina.
DAGA Shafin: Rariya
Hon. Abdulrazaq Dahiru Kaita, wanda yake shugabantar ƙungiyar tafiyar Matasan Katsina (The Movement Forum), ya jaddada cewa suna ci gaba da nazari mai zurfi da tsare-tsare kan yadda za su kafa sabuwar Najeriya da ma jihar Katsina a kan dora shugabanci a ƙarƙashin tafiyar Matasa.
Ya bayyana haka a lokacin taron Manema Labarai ranar Talata 24 ga watan Nuwamba 2024, inda ya ce, za su ci gaba da tsare-tsare na ganin sun yi hulɗa da sauran ƙungiyoyi masu aƙida irin ta su a ciki da wajen jihar Katsina, domin ganin sun yi nasara a kan zaɓar Matasa zallah a 2027.
A cikin jawaban Hon. Kaita, ya ce a jihar Katsina da ma Nijeriya an maida Matashi bawa a siyasa duk da sai da shi ake amfani wurin yaƙin neman zaɓe, tare da yin amfani da shi wajen ganin an yi nasara, amma da an ci zaɓe ba a ƙara ganin darajar sa sai wata kakar zaɓen.
Shugaban ya jaddada cewa, a matsayin sa na shugaban ƙungiyar na jihar Katsina, zai jajanta ma kowanne Matashi na ƙasar nan wurin alhini da nuna damuwar sa bisa halin da s**a wayi gari a ciki, a matsayin su na Matasa, waɗanda ba a son su yi shugabancin ƙasar duk da halin da ƙasar ke ciki a yanzu irin shugabancin Matasa take so.
Kazalika, ya ce amma duk da haka matashin Najeriya ba shi da wata dama gameda tsarin shugabanci da shuwagabannin s**a tanadar ma su, ta dalilin haka ne s**a yanke shawarar kafa ƙungiyar tun a ranar 15 Agusta, 2024, domin yin fafutuka ga matasan jihar Katsina da ma Najeriya.
Ya nanata cewa, su matasan Najeriya sun daina bautar kowa a harakar siyasa sai 'yan uwansu kaɗai Matasa, shiyasa ma tunda farko s**a fice daga kowacce jam'iyya, wanda yana ɗaya daga dalillan da yasa s**a fice daga Jam'iyyu daban-daban domin su zo su tsira wata jam'iyya mai k**a da ta Matasa.
Daga ƙarshe, ya jawo hankalin duk masu ruwa da tsaki na Matasan jihar Katsina, tun daga
'yansiyasa, masu Ilimi na Addini da na Zamani, 'yankasuwa da kuma masu jini a jika, a kan kowa ya farka su tashi tsaye domin ganin cewar sun maido martaba da darajar Nijeriya.
AUDU BULAMA BUKARTI
Abba Hikima
Kunga Yanda Wannan Tafiyar Take 'Kara 'Karbuwa A Wajen Mutanen Nigeria Ko! Mudai Fatan Mu Allah Yabamu Sa,a Rabo.