18/11/2024
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kira ga Majalisar ƙasa ta yi watsi da duk wani Yunkuri da zai yi wa Arewa rashin adalci ta hanyar dokokin gyaran haraji da ake son samarwa.
Kwankwaso ya yi wannan magana ne ranar Lahadi a wajen bikin kammala karatu na Jami’ar Skyline da aka gudanar a Cibiyar Ammani, GRA Nasarawa, Kano.
A cikin jawabin nasa, Kwankwaso ya zargi Lagos da kokarin mallake yankin Arewa. Ya ce akwai yunkuri mai yawa daga bangaren Lagos na neman mamaye Arewa ta hanyoyi daban-daban.
Ya kuma zargi Shugaban Ƙasa, wanda ya fito daga Lagos, da yin katsalandan a batun sarautar Kano.
Kwankwaso ya yi kira ga Majalisar Ƙasa da ta kare martabar Arewa da tattalin arzikinta ta hanyar hana aiwatar da duk wani tsari da zai kawo wa yankin asara ko rashin adalci.
Ya kamata shugabanni su yi aiki don kare muradun mutanen Arewa, maimakon barin wasu daga sauran bangarorin ƙasa su yi yunkurin tauye mana ‘yanci da martaba,"** in ji shi