Isa Yahuza

Isa Yahuza Beuty is nothing when the brain is empty

08/09/2022

HADISI NA DAYA. An karbo daga sarkin muminai Abi Hafs Umar dan Khadhab Allah Madaukakin sarki ya yarda dashi yace: naji manzon Allah s.a.w yana cewa “Ayyuka kawai sun dogara da niyyoyi, kuma ko wane mutum yana da abinda yayi niyyarsa, wanda hijirarsa ta kasance domin Allah da manzonsa to ladar hijirarsa tana ga Allah da kuma manzonsa, wanda hijirarsa ta kasance domin duniya don ya sameta ko kuma wata mata da yake son ya aura, to ladar hijirarsa tana akan abinda yayiwa hijira. Shuwagabannin ma ruwaitan hadisi s**a ruwaitoshi, Abu Abdullah Muhammad dan Ismail dan Ibrahim dan Mugira dan Bardizba Al-Buhariyyu, da Abu Hussain Muslim dan hajjaj dan Muslim Al-Qushairiyyu Al-Naisaburiyyu, a cikin Ingantaccen Littafinsu wadanda sune Littafinsu yafi wallafa (hadisi ingantacce).

HUKUNCIN SHAQAR TURARE (NA FESAWA DANA KONAWA)– Tambaya: Shin ya halatta ga mai azumi ya shanshana kamshin turaren fesaw...
25/04/2021

HUKUNCIN SHAQAR TURARE (NA FESAWA DANA KONAWA)

– Tambaya: Shin ya halatta ga mai azumi ya shanshana kamshin turaren fesawa ko na gaushi da ake konawa?

– Amsa: Mai azumi ba zai shaqi turaren wuta (Uud) ba, amma sauran turare waxanda ba na konawa ba, to babu laifi akansu, Amma turaren uud kam ba zai shanshane shi ba; saboda wassu maluma suna ganin cewa wannan turaren yana karya azumi idan mai yinsa ya shake shi; saboda ya kan tafi zuwa ga kwakwalwa, kuma tafiyat tasa ta kan zama da karfi, Amma da zai shake shi ba tare da nufi ba to ba zai karya masa azuminsa ba.

– Tambaya: Shin a cikin yinin ramadhana ya halatta ya yi amfani da ti**re, misali: turaren uud na mai da ake shafawa, da koloniya, da kuma turaren gaushi da ake konawa?

– Amsa: A, ya halatta, da sharadin kada ya shaki turaren gaushi da ake konawa.



HUKUNCIN AMFANI DA TOZALI, DA KAYAN KWALLIYA A CIKIN YININ RAMADHANA

– Tambaya: Menene hukuncin amfani da tozali ko wasu kayan kwalliya ga mata a cikin yinin ramadhana, kuma shin yana vata azumi ko a’a?

– Amsa: Tozali baya karya azumin ‘ya mace, ko na namiji, a mafi ingancin zance guda biyu na maluma, a kowani irin hali. Saidai kuma ayi amfani da shi da daddare shi ya fi dangane da mai azumi mace ko namiji. Haka kuma abubuwan da mata ke ado da su na sabulu ko mayuka, ko makamancin haka na dangin abubuwan da su ke alaka da fata kawai, misalin su kunshi (lalle), da kayan barbade-barbade da makamantan haka, dukkan wadannan babu laifi ga mai azumi mace, ko namiji su yi amfani da shi, tare da cewa baya halatta a yi amfani da kayan shafe-shafe matukar zai cutar da fiska (kamar canza mata kala). Allah ne majibincin dacewa

Assalamu alaikum wa rahama tullahi wabara katuhu An karɓo daga Umar (R.A) ya ce, "Yayin da muna zaune a wurin Annabi (ﷺ)...
23/01/2021

Assalamu alaikum wa rahama tullahi wabara katuhu An karɓo daga Umar (R.A) ya ce, "Yayin da muna zaune a wurin Annabi (ﷺ) wata rana, sai wani mutum ya bayyana gare mu, mai tsananin farin tufafi, mai tsananin baƙin gashi, kuma ba a ganin alamun tatiya tare da shi, kuma a cikinmu babu wanda ya san shi, har ya zauna kusa da Annabi (ﷺ) ya jingina gwiwowinsa guda biyu zuwa ga gwiwowin Annabi (ﷺ), ya ɗora tafukan hannunsa a kan cinyoyinsa, sai ya ce, "Ya Muhammad! Ba ni labari game da musulunci." Sai Annabi (ﷺ) ya ce, "Muslunci, shi ne ka shaida babu abin bautawa bisa ga cancanta, sai Allah, kuma Muhammad (ﷺ) Manzon Allah ne, ka tsayar da sallah, ka ba da zakka, ka yi azumin watan Ramadan, ka ziyarci ɗakin Allah in ka sami iko." Sai ya ce, "Ka yi gaskiya!" Sai muka yi mamakinsa, saboda yana tambayarsa, kuma yana gasgata shi. Sai ya ce, "Ba ni labarin Imani." Sai ya ce, "Ka yi imani da Allah, da Mala'ikunsa da Littattafansa, da Manzanninsa da ranar lahira, kuma ka yi imani da ƙaddara alherinta da sharrinta." Sai ya ce, "Ka yi gaskiya!" Sai ya ce, "Ba ni labarin kyautatawa." Ya ce, "Ka bauta wa Allah kamar kana ganinsa, idan ba kaganinsa, to shi yana ganinka." Ya ce, "Ba ni labarin alƙiyama." Sai ya ce, "Wanda aka tambaya, bai fi mai tambayar sani ba." Sai ya ce, "Ba ni labarin alamominta." Sai ya ce, "Baiwa ta haifi uwargidanta, kuma ka ga mutane marasa takalma, matsiraita, talakawa, masu kiwon dabbobi, suna tsawaita gine-gine." Sai (mutumin), ya tafi, muka zauna lokaci mai tsawo, sannan sai Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "Ya Umar! Ko ka san mai tambayar nan? Sai na ce, "Allah da Manzonsa su ne s**a sani" Sai ya ce, "Haƙiƙa Jibrilu ne ya zo muku don ya koya muku addininku." Muslim ne Ya rawaito shi

Address

Gidan Dare
Sokoto

Telephone

+2348059729379

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Isa Yahuza posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Isa Yahuza:

Share