18/09/2023
Kasar Saudi Arabia ta bada umarnin dakatar da karantar da littafan wahabiyannci dake koyar da tsatstsauran ra'ayin addinin musulunci tare da bada umurnin a fitar da littafan daga cikin masallatan kasar.
Ministan harkokin addinin musulunci na kasar Saudi Arabia, Sheikh Abdullatif Al-Sheikh shine ya bada wannan umurni ga malamai da limaman masallatai na kasar, inda yace a daina karantar da littafan domin rage kaifin akidar wahabiyannci.
Jaridar Saudi Gazette ta rawaito cewa Sheikh Abdullatif ya dakatar da yiwa wadanda ba musulmi ba da'awa ba tare da sahhalewar hukumomin kasar Saudi Arabia ba kuma za'a hukunta duk wani malami da aka samu da wuce gona da iri wajen kira ga addinin musulunci.
Daukar wannan mataki a kasashen Musulmi shine zaikawo Karshen ta'addanci da akesamun wasu tsurarun musulmi nayi da sunan jahadi.
Kasashe da dama kamar masar sun dau irin wannan mataki daga lokacin s**a samu zaman lafiya, muna fatan kasarmu Nigeria zatayi koyi da irin wanan mataki domin Boko Haram kadai ta isa misali.