17/04/2026
MAL. YA DAWO KAN
SHAWARAR KWAMARET..........
Lokaci ya yi da zan fito fili na bayyana abin da ya dade yana damuna a zuciya.
Duk wanda ya san kwamaret sani salisu darma a kafafen sada zumunta, musamman a bangaren siyasa, ya san na dade ina cikin tafiyar gidan malam ibrahim shekarau.
Soyayyar da nake yi masa ce ta sa na tsunduma harkokin siyasa tun daga social media har zuwa grassroots.
Tun bayan kammala mulkinsa a matsayin gwamnan kano har zuwa zaben 2023, na kasance tare da shi cikin duk wata tafiya da gwagwarmaya.
Sai dai dalilin da ya jawo rabuwata da wannan tafiya shi ne hadewarsa da tsohon gwamnan kano, rabiu musa kwankwaso, a karkashin jam’iyyar NNPP.
A wancan lokaci, Nayi rubuce Rubuce na bayar da shawara cewa wannan hadaka ba za ta dore ba, saboda akwai kiyayya da rikicin siyasa a tsakanin bangarorin biyu.
Amma ba a dauki wannan shawara da muhimmanci ba, har aka rufe ido aka ci gaba da tafiya, lamarin da ya kai ga s**a da kalubale a kaina daga wasu bangarorin tafiyar.
Sai ga shi k**ar yadda nayi hasashe, kafin kammala zaben 2023 hadakar ta watse, aka rabu a siyasa, abin da ya kara tabbatar da abin da na fada Zai faru tun farko.
Yanzu kuma da ake tunkarar zaben 2027, na ga alamun malam shekarau na kokarin komawa jam’iyyar APC, wacce a ganina ita ce mafi dacewa da tafiyar siyasarsa tun 2023.
A lokacin mulkin gwamna abdullahi umar Ganduje an rararshi Malam akan Kada ya fita daga APC , an bawa malam damar siyasa mai yawa, har ma da dama a matakan takara da wakilci a sassa daban-daban na kano.
Na bar tafiyar gidan malam ba tare dana sanar da duniya ba, amma Allah ya san niyya, kuma ya hada ni da wadanda s**a fahimci darajarta da abin da zan iya a siyasa, s**a gayyace ni tafiyar su.
Tambayar da ke a nan ita ce: idan malam ya dawo APC a yanzu, shin zai sake samun irin damar da ya taba samu a baya?
na barku lafiya.
17/4/2026