22/08/2026
Wani sabon bayani da Maikano Sorondinki ya wallafa ya jawo hankali kan makomar Durbar Mauludi da rikicin masarautar Kano.
A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Mai Kano Sorondinki ya bayyana cewa akwai bayanan da ke nuna cewa Mai Martaba Sanusi Lamido Sanusi na shirin gudanar da jerin gwanon Durbar Mauludi a Kano a ranakun Litinin 24 da Talata 25 ga Agusta 2026.
A cewarsa, wannan shiri ya biyo bayan wasu shirye-shirye da ake zargin Mai martaba sarkin Aminu Ado Bayero ya yi na gudanar da Durbar a ranakun.
Mai Kano Sorondinki ya kuma yi ikirarin cewa Sanusi Lamido Sanusi ya tattauna da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, inda aka ba shi damar gudanar da wannan shiri.
Bugu da ƙari, rubutun ya yi zargin cewa ɓangaren Kofar Kudu na shirin tattaro magoya baya daga ƙananan hukumomi 44 na jihar domin gudanar da zanga-zanga kan Matsayin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA), bisa zargin goyon bayan Aminu Ado Bayero da samar masa da tsaro.
Sai dai, Gambiza Tv ta jaddada cewa waɗannan bayanai zarge-zarge ne da ke cikin rubutun Mai Kano Sorondinki, kuma ya kamata a jira tabbacin hukumomin da abin ya shafa kafin ɗaukar su a matsayin tabbataccen lamari.
Mai Kano Sorondinki ya kuma yi kira ga magoya bayan Sarkin kano Alh Aminu Ado Bayero da su kasance cikin taka-tsantsan, tare da guje wa duk wani mataki da zai iya haifar da rikici ko tashin hankali.
A ra'ayinku, ya kamata hukumomin tsaro su ɗauki waɗanne matakai domin hana rikici tsakanin magoya bayan ɓangarorin masarautar Kano?
Domin samun ƙarin labaran Kano, siyasa da sauran muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya, ku ci gaba da bibiyar Gambiza TV.