10/04/2026
Marigayi Dr. Rilwanu Lukman:
Babban masanin tattalin arziki da man fetur wanda ya kafa tarihin da ba za'a taba mantawa dashi ba a Najeriya da ma duniya baki daya.
An haife shi a ranar 26 ga watan Agusta, 1938 a birnin Zariya dake Jihar Kadunan Najeriya.
Ya fito daga gidan mutunci da ilimi a masarautar Zazzau.
Dr. Rilwanu Lukman ya kasance babban kwararren Engineer wanda yayi karatu a manyan makarantun duniya:
*Bayan kammala karatun firamare ya wuce zuwa Kwalejin Gwamnati ta Zariya wato Barewa College Inda yayi karatun sakandare.
A Kwalejin Fasaha ta Zariya (yanzu ABU Zaria): Ya fara karatunsa na gaba da sakandare.
*Sannan ya wuce Imperial College London, Inda ya sami digirinsa na farko a fannin hakar ma'adanai (Mining Engineering).
*Daga nan ya wuce University of Mining and Metallurgy (Austria), Yayi karatu a fannin hakar ma’adanai.
*Sannan ya wuce McGill University (Canada), inda ya kara samun horo na musamman a fannin sarrafa ma'adanai.
*Sannan sai Digirin Digirgir (PhD):* Inda ya sami lambobin girma na digirin digirgir (Doctorate) daga jami'o'i daban-daban saboda kwazonsa.
Ya rike manyan mukamai wadanda kadan ne 'yan Najeriya s**a taba rikewa ya fara rike:
Ministan Ma'adanai da Lantarki a shekarar (1984–1985).
Ministan Man Fetur, Ya rike wannan mukamin sau biyu (1986–1989 da kuma 2008–2010).
Ministan Harkokin Waje daga shekarar (1989–1990).
Sannan ya zama Sakatare Janar na Kungiyar OPEC ta duniya, Shine dan Najeriya na farko kuma daya daga cikin mutanen da s**a fi dadewa suna jan ragamar kungiyar kasashen dake fitar da man fetur (OPEC) a duniya tsakanin 1994 zuwa 2000.
Ya taba zama mashawarci na musamman kan harkokan man fetur ga Shugaba Olusegun Obasanjo.
😭😭😭😭
Rasuwa.
Dr. Rilwanu Lukman ya riga mu gidan gaskiya a ranar *21 ga watan Yuli, 2014, Ya rasu yana da shekaru 75 a duniya bayan gajeriyar jinya a birnin Vienna na kasar Austria, inda yake zaune lokaci zuwa lokaci saboda ayyukansa na kasa da kasa.